fidelitybank

Gwamnatin Kano za ta daura kafar wando daya da Sharar Bola

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da wani gagarumin shirin yaƙi da matsalar shara da ke addabar sassan birnin.

Shirin na haɗin gwiwa da ma’aikatun ciniki da sufuri zai tabbatar da kwashe sharar da ta cika wuraren da ake tattara ta a kasuwanni da kuma unguwanni.

Jihar Kano na cikin jihohin da matsalar shara ke ci gaba da barazana a tituna da kuma unguwanni inda a wasu wuraren hayaƙin da ake kona bolar ke mummunar barazana ga jama’a.

Ma’aikatar kula da muhalli ta jihar Kano ta tabbatar da cewa aikin kawar da sharar zai gudana ne ƙarƙashin wani shirin haɗin gwiwa na kar-ta-kwana wanda zai tabbatar da cewa tulin sharar da ake fama ta shi a sassan jihar an kawar da shi cikin ƙanƙanin lokaci.

Kwamishinan ma’aikatar, Dr Dahiru Muhammad Hashim ya ce yanzu aiki an faro shi daga kasuwanni zuwa cikin unguwanni.

“Akwai abubuwa da dama da gwamnati ba za ta ci gaba da lamunta ba don tabbatar da tsaftar muhalli da kare lafiyar al’umma.”

Bu-gu-da-kari Dr Dahiru Muhammad Hashim ya ce za su gayyato kamfanoni su zuba jari a harkar sarrafa shara, ta yadda jama’a za su daina kallon ta a matsayin shara, maimakon haka su kalleta a matsayin wani abu da za a iya samun arziki a cikinsa.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp