fidelitybank

Gwamnatin Kano za ta daura kafar wando daya da Sharar Bola

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da wani gagarumin shirin yaƙi da matsalar shara da ke addabar sassan birnin.

Shirin na haɗin gwiwa da ma’aikatun ciniki da sufuri zai tabbatar da kwashe sharar da ta cika wuraren da ake tattara ta a kasuwanni da kuma unguwanni.

Jihar Kano na cikin jihohin da matsalar shara ke ci gaba da barazana a tituna da kuma unguwanni inda a wasu wuraren hayaƙin da ake kona bolar ke mummunar barazana ga jama’a.

Ma’aikatar kula da muhalli ta jihar Kano ta tabbatar da cewa aikin kawar da sharar zai gudana ne ƙarƙashin wani shirin haɗin gwiwa na kar-ta-kwana wanda zai tabbatar da cewa tulin sharar da ake fama ta shi a sassan jihar an kawar da shi cikin ƙanƙanin lokaci.

Kwamishinan ma’aikatar, Dr Dahiru Muhammad Hashim ya ce yanzu aiki an faro shi daga kasuwanni zuwa cikin unguwanni.

“Akwai abubuwa da dama da gwamnati ba za ta ci gaba da lamunta ba don tabbatar da tsaftar muhalli da kare lafiyar al’umma.”

Bu-gu-da-kari Dr Dahiru Muhammad Hashim ya ce za su gayyato kamfanoni su zuba jari a harkar sarrafa shara, ta yadda jama’a za su daina kallon ta a matsayin shara, maimakon haka su kalleta a matsayin wani abu da za a iya samun arziki a cikinsa.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp