fidelitybank

Gwamnatin Kano Tinubu ya ce har yanzu ni ne shugaban APC – Ganduje

Date:

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa wanda mazaɓarsa ta ce ta dakatar da shi, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin Jihar Kano ba ta isa ta ƙwace kujerarsa ba, yana mai cewa shugaban ƙasa Bola Tinubu da kansa ne ya tabbatar masa cewa “kujerarsa na nan daram-dam.

Ganduje ya bayyana haka ne a wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke nuna shi yana jawabi ga dandazon magoya bayansa da suka kai masa ziyara a gidansa na Abuja domin nuna goyon baya.

Ya ce “jiya na ga shugaban ƙasa, Bola Tinubu kuma na yi masa bayanin komai kuma ya gode muku abin da kuka yi.” in ji Ganduje yayin da yake magana ga magoya bayansa.

“Sannan shugaban ya ce ku yi hakuri, wannan kujerar da suke hari, kujerar tana nan ta zauna daram-dam.” in ji Ganduje.

Tsohon gwamnan ya kuma ce Tinubu ya tabbatar masa da cewa kujerar shugabancin jam’iyyar APC ta Najeriya tasa ce kamar yadda ya faɗa “kujerar shugabancin APC ta Najeriya tana kan Abdullahi Umar Ganduje.”

An nuna magoya bayansa a cikin bidiyon suna ta murna da shewa da tafi yayin da tsohon gwamnan ke gabatar da kalamansa.

A yau Laraba ne dai wata babbar kotu a jihar Kano ta dakatar da Ganduje daga shugabancin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya bayan wasu shugabannin APC tara a mazaɓar ta Ganduje suka shigar da ƙara kan a dakatar da shi bayan wata takardar koke da wani ɗan jam’iyyar Ja’afaru Adamu ya shigar.

A takardar koken, Adamu ya yi magana kan tuhume-tuhumen rashawa da ake yi wa tsohon gwamnan inda ya buƙaci jagororin mazaɓar su gudanar da bincike kan batun domin farfaɗo da ƙimar jam’iyyar da kuma tasirin da batun zai yi a fafutukar gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta yaƙi da rashawa.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp