fidelitybank

Gwamnatin Kano ta ɗaukaka ƙara akan ta biya ƴan kasuwa diyyar biliyan 30 na rusau

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta daukaka kara kan hukuncin da wata babbar kotun tarayya ta yanke na cewa ta biya diyyar Naira biliyan 30 ga wasu ‘yan kasuwar da suka rusa shagunansu.

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano karkashin jagorancin mai shari’a Simon Anogede, a lokacin da ta ke yanke hukunci a shari’ar da kungiyar ‘yan kasuwa ta shigar, ta ce abin da gwamnati ta yi na zalunci ne da kuma saba wa kundin tsarin mulkin kasar.

Sai dai kotun ta bada diyyar Naira biliyan 30 ga ‘yan kasuwar, maimakon Naira biliyan 250 da suka nema daga gwamnati.

Alkalin ya bayar da umarnin a biya kudin nan take.

Sai dai gwamnatin jihar Kano ta ce, ta daukaka kara kan hukuncin da ta bayyana a matsayin rashin adalci.

Babban Lauyan Jihar kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Barista Haruna Isa Dederi, ya bayyana cewa, kotu ba ta yi daidai ba wajen yanke hukunci ga kungiyar ‘yan kasuwa saboda dokar amfani da filaye ta fito karara kan matsayin filaye a kowace jiha.

Ya dage cewa kotu ba ta da hurumin ko da sauraren karar saboda gwamnati ce kadai ta mallaki fili kamar yadda dokar amfani da filaye ta tanada.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp