fidelitybank

Gwamnatin Kano ta yi gargadi a kan tirka-tirkar Tik-Tok da a ke yi

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta yi wa Malaman addinin Musulunci gargadi da masu amfani da shafukan sada zumunta da su lura da abin da suke faɗa, domin harshe ka iya kai su ya baro su.

Cikin wani hoton bidiyo na minti biyar da kwamishinan addinai na jihar Muhammad Tahar Adam Baba Impossible ya yi, ya bayyana matsayar gwamnatin Jihar Kano kan ce-ce-ku-cen da ya ɓarke bayan yaɗuwar wani bidiyo da Sheikh Daurawa ke magana a kan al’aurar mata da kuma martanin da Nafisa Ishak wata mai amfani da shafin Tiktok ta yi.

A makon da ya gabata ne Sheikh Daurawa a wani bidiyo aka ji yana ba da misali da yadda al’aurar mata ke da muni duk da cewa yana cikin ƙwace-ƙawacen duniya.

Hakan ya sa mutane suka yi ta mayar da martani daga ɓangarori daban-daban, sai dai mafi jan hankali shi ne na wata mai amfani da shafin Tiktok Nafisa wacce ta yi “kakkausan martani” ga Malam Daurawan.

Daga baya kuma wani malamin mai suna Asadus Sunnah ya yi nasa bidiyon yana gargaɗin Nafisan tare da yin barazanar cewa suna da yaran da za su tura su yi maganinta.

Kwamishinan addinan ya shaidawa BBC abin da ya sa gwamnati ba ta yi magana tun da farkon lamarin ba, saboda ta tsaya tattara bayanai ne daga ɓangarorin kafin yanke hukunci.

Baba Impossible ya fara da bayani ne kan cewa Malam Daurawa bai yi dai-dai ba kan bayanan da ya yi, yayin wani karatu a ranar Litinin wanda yake yi kullum.

“Gwamnatin jihar Kano ta ji ta kuma saurari abubuwan da ke faruwa duka, ta tambayi malamai da masana, an kuma ji bangarori daban-daban kuma an kalli jawabin kowa.

“Abin da ma’aikata ta tsaya a kansa, kamar yadda muka ji daga bakin malamai, shi mai jawabi na farko ya yi kuskure a jawabinsa, kamata ya yi ya tsaya kan Ƙala Allahu ƙala Rasulihi.

“Idan akwai wani ƙarin bayani kar a yi shi cikin yadda zai yamutsa hazo yadda zai ta da ƙura, yadda zai tayar da hankalin mutane yadda zai zama kamar akwai batsa, kamar akwai cin mutunci, kamata ya yi a saya shi.

“Don haka tun a nan muka fuskanci akwai kuskure a jawabin da ya yi,” in ji Baba Impossible.

Ya ci gaba da cewa malami ba ma’asumi ba ne zai iya yin kuskure, don haka idan malami ya yi kuskure ya iya gyarawa.

Cikin bayanansa ya riƙa kin ambatar sunan Malam Aminu Daurawa, inda ya riƙa siffanta shi da mai magana na farko ko kuma mai wa’azi.

Da yake bayani a kan Nafisa Ishak, Kwamishinan ya ce ita ma a jawabanta akwai kuskure masu yawa kuma sun yi nazari kansu.

“Ba ta cikin rukunin wadanda za su iya mayar wa da Malamin martani, idan malami ya yi maganar malami dan uwansa ya kamata ya mayar masa da martani idan da kuskure ya fada masa cewa bai yi dai-dai ba ya gyara.

“Amma ba ita da take matar wani ko budurwa ko bazawara ba.

“Maganganun da ta yi sun yi tsauri, don haka ba mu yarda da abin da ta fada ba, ba dai-dai ba ne, ko da yake dai ba zagi ba ne kai tsaye, amma zagi ne idan aka kalli yadda ta furta su,” in ji Kwamishinan addinan.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp