fidelitybank

Gwamnatin Kano ta sassauta dokar hana fita

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta sassauta dokar hana zirga-zirga a jihar daga karfe shida na safe zuwa karfe shida na yamma.

Wannan dai na daga cikin abubuwan da aka tattauna ya yin taron majalisar koli ta harkokin tsaron jihar da aka yi a yau Talata karkashin jagorancin gwamnan jihar.

A gefe guda kuma an bude manyan kasuwannin jihar na wucin gadi, inda aka yi hada-hada daga safe zuwa karfe daya na rana.

An sanya dokar hana fitar ne, a ranar Alhamis din ta wuce, wato ranar da aka fara zanga-zangar matsin rayuwa a fadin kasar, sakamakon rikidewar da zanga-zangar ta yi ta koma tarzoma.

Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, ne ya sanar da saka dokar ce ta tsawon awa 24 bayan wasu ɓata-gari sun farfasa tare da wawashe kayayyaki a shagunan ‘yan kasuwa da gine-ginen gwamnati yayin zanga-zangar.

Ƙarin abin da ya ta’azzara al’amuran na Kano shi ne yadda maƙwabtan jihohi na Kaduna da Katsina da Jigawa suka saka dokar hana fitar, duka saboda tarzomar ɓata-garin.

Daga bisani an sassauta dokar, inda aka mayar da fita harkoki daga karfe 8 na safe zuwa biyu na rana.

Jihar Kano na cikin wuraren da zanga-zangar ta fi rikiÉ—ewa zuwa tashin hankali, inda rahotonni ke cewa an kashe mutane da dama.

Sai dai har kawo yanzu babu wasu alƙaluma daga gwamnati ko ‘yan sanda na yawan waɗanda suka mutu.

A ranar Litinin ma – rana ta biyar – masu zanga-zangar sun fita wasu titunan birnin ɗauke da tutocin Rasha, yayin da rundunar ‘yan sandan jihar ta ce tana ci gaba da bin sawun kayayyakin da aka sace.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp