fidelitybank

Gwamnatin Kano ta sallami ‘yan Jaridu 14

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da ‘ƴan jarida 14 da ke aiki a fadar gwamnatin jihar daga aiki tare da neman sauyinsu daga hukumomin da suke ƙarƙashinsu.

A wani saƙo da kakakin gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ga waɗanda abin ya shafa, ya umarce su da su koma wuraren aikinsu, tare da neman hukumominsu su aika da wasu da za su maye gurbinsu a gidan gwamnatin jihar.

Babu wani dalili da kakakin ya bayyana na ɗaukar wannan mataki, illa dai ya buƙace su da su bi umarnin wanda ya fara aiki daga yau Talata.

To amma a saƙon da ya rubuta a shafin WhatsApp na tawagar ‘yanjaridar da ke aiki a fadar gwamnatin jihar ta Kano, Sanusin ya bayyana cewa : ”Abin takaici a lokacin da na yi tafiya zuwa ƙasar Serbia a makon da ya gabata, wasu abubuwa sun faru, saboda haka akwai buƙatar shugabancin a wannan mawuyacin hali ya ɗauki mataki…”

Wasu daga cikin ƴanjaridar da abin ya shafa sun haɗa da na kafofin yaɗa labarai na gwamnatin jihar da na tarayya da kuma masu zaman kansu.

Daga cikinsu akwai daraktan wayar da kan al’umma, Aliyu Yusuf da jimi’im hulda da jama’a, Sani Suraj Abubakar da Adamu Dabo da ke kai rahoto ga gidan rediyon Pyramid (FRCN). Sai kuma Naziru Yau daga ARTV da Sadiq Sani AA daga ARTV da Rabiu Sunusi da Umar Sheka daga rediyon Freedom, cewar Premium Times. Har ila yau, akwai Jabir Dan’abba daga gidan rediyon Nasara sai Labara Sound da Simon daga AIT sai Nasiru Danhaki daga NTA da direbansu, Abdullahi Sule da Murtala Baba Kusa daga gidan rediyon Express da Ibrahim Muazzam daga rediyon Kano.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp