fidelitybank

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Date:

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake, tabbatar da kudurin gwamnatinsa na karfafa matasa ta hanyar samar da ayyukan yi masu ɗorewa, fadada damar koyon sana’o’i, da kuma ƙarfafa yaki da amfani da miyagun kwayoyi.

Gwamnan ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Laraba, domin tunawa da Ranar Matasa ta Duniya a wannan shekara.

“Matasa su ne ginshiƙin canjin tattalin arziki da zamantakewa a Kano,” in ji Gwamna Yusuf. “Mun sake buɗe cibiyoyin koyon sana’o’i a fannoni daban-daban, wanda hakan ya ba dubban matasanmu damar dogaro da kansu.”

Haka kuma, an samar da damar aiki kai tsaye a muhimman sassa kamar kiwon lafiya, ilimi, aikin gona, da ayyukan gwamnati.

Gwamnan ya kuma bayyana shirin sake buɗe Cibiyar Gyara Hali na Kiru domin gyara da dawo da matasa masu laifi musamman waɗanda ke fama da amfani da miyagun kwayoyi.

A bangaren Fasahar Sadarwa da Kwamfuta (ICT), Yusuf ya jaddada nasarorin da aka samu ta kafuwar Hukumar KASITDA da kuma nasarar shirya Taron Kasa da Kasa kan Fasaha da Kwamfuta.

Ya bayyana waɗannan a matsayin muhimman matakai don sanya Kano cibiyar ƙirƙira da kwarewar dijital.

“A wannan Ranar Matasa ta Duniya, muna murnar juriya, ƙirƙira, da ƙarfin matasanmu,” in ji gwamnan. “Gwamnatina za ta ci gaba da zuba jari a makomar su ta hanyar samar da ayyukan yi, ilimi, fasaha, da yaki da miyagun kwayoyi.”

Gwamna Yusuf ya yi kira ga shugabannin al’umma, malamai, iyaye, sassan masu zaman kansu, da sauran masu ruwa da tsaki su haɗa kai wajen samar da yanayi mai aminci, haɗin kai, da wadata domin matasan Kano su cika burinsu cikin cikakken iko.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...

An kaiwa Malamin addini hari a Kano bayan an jikatasu da Matarsa

Wani malamin addinin Musulunci, Malam Kabir Idris, da matarsa...

Kotun Kano ta daure wata Mata da ake zargin ta tsafe su

Kotun Majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland, ƙarƙashin...

Dalibi ya kashe kansa a cikin Jami’a

Hukumar jami'ar Obafemi Awolowo da ke jihar Osun, sun...

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...
X whatsapp