fidelitybank

Gwamnatin Kano ta kai Buhari kotu akan sauyin kudi

Date:

Gwamnatin Jihar kano ta kai gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari kara a gaban Kotun Kolin kasar nan, a kan sauyin fasalin wasu daga cikin manyan kudin kasar na naira 200 da 500 da 1,000.

A karar wadda Babban Lauyan jihar ta Kano ya shigar ta hannun Sunusi Musa babban lauya a Najeriya (SAN), a jiya Alhamis, gwamnatin tana bukatar kotun ta ayyana cewa Shugaba Muhammadu Buhari shi kadai ba shi da hurumin umartar Babban Bankin Kasar, CBN ya dakatar da amfani da takardun kudin na naira 200 da 500 da kuma 1,000 ba tare da tuntuba da amincewar majalisar tattalin arziki da kuma majalisar zartarwa ta kasar ba.

A don haka ne gwamnatin jihar ta Kano take son Kotun ta soke matakin Babban Bankin na Najeriya na janye takardun kudaden saboda abin ta kira wahalar da al’ummar jihar ke ciki asaboda matakin na CBN.

A tattaunawarsa da BBC lauyan da ya shigar da karar Sunusi Musa ya ce a ranar Laraba ne Kotun za ta saurari karar.

Harwayau gwamnatin tana son kotun ta bayar da umarnin da zai tilasta wa gwamnati ta soke shirin nata na sauyin kudi saboda a cewarta ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar na 1999.

A karar gwamnatin jihar ta Kano tana kuma bukatar Kotun Kolin ta zartar cewa umarnin da Shugaba Buhari ya bai wa Babban bankin Kasar na takaita yawan kudin da jama’a za su fitar daga asusunsu na banki ba tare da tuntubar majalisar tattalin arziki da kuma ta zartarwa ba, abu ne da ya saba wa tsarin mulki da saba wa doka a don haka ba shi da iko.

Kafin wannan daman gwamnonin jihohin Kaduna da Zamfara da Kogi sun shigar da kara kan batun, har Kotun Kolin ta dakatar da Babban Bankin Najeriyar aiwatar da wa’adin da ya sa na daina amfani da takardun kudin na ranar 10 ga watan nan na Fabarairu wato yau, Juma’a, har sai ta yanke hukunci a ranar 15 ga watan na Fabarairu na 2023.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa Æ´an wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta...

Yansanda sun kama Sojoji cikin ‘Æ´an Æ™ungiyar asiri’ a jihar Ogun

Rundunar 'yansanda reshen jihar Ogun, ta tabbatar da kama...

Yadda ambaliya ta shanye Adamawa

Rahotonni daga birnin Yola na jihar Adamawa na cewa,...

Yadda Jodan da Dubai ke jefa wa al’ummar Gaza abinci ta sama

Kafar yaÉ—a labarai ta gwamnatin Jordan ta ce, jiragen...

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar É—an wasan...
X whatsapp