Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da wani gagarumin shirin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a yankunan karkara, wanda zai shafi al’umomin karkara sama da 100 a fadin jihar.
Shirin wanda Shenzhen Lemi Technology Development da Lemi Renewable Electricity Limited suka kafa, na neman samar da na’urorin samar da hasken rana ga kananan al’ummomin karkara.
Da ya ke kaddamar da shirin a Kano, Kwamishinan Raya Karkara da Raya Al’umma, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya ce aikin zai kuma samar da guraben ayyukan yi ga dimbin matasa a fadin jihar tare da bunkasa zamantakewa da tattalin arzikin mazauna karkara.
Ya ce,”Domin cimma manufofin da aka gindaya, gwamnatin jihar Kano ta kulla yarjejeniya da kamfanin na samar da kayayyakin amfani da hasken rana.
“Shirin gwamnatin jihar na samar da dukkanin abubuwan more rayuwa da a ke bukata a fadin kananan hukumomin 44”. In ji Musa Iliyasu.
A nasa jawabin shugabar kamfanin Shenzhen , Monica Liang, wadda ta sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna, ta ce, kamfanin zai samar da na’urori masu dorewa da inganci aikin.