fidelitybank

Gwamnatin Kano ta kaddamar da kwamitin gudanar da Hisbah

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta amince da kundin tsarin mulki na kwamitin mutane 22 da za su tafiyar da harkokin hukumar Hisbah ta jihar.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Malam Muhammad Garba, wanda ya bayyana hakan a cikin sanarwar, ya ce, amincewar ta biyo bayan shawarar kwamitin da aka kafa, domin duba ayyukan hukumar da kuma yin daidai da dokar jihar.

Ya ce. rahoton kwamitin ya ba da shawarar kafa hukumar kuma an gabatar da shi a gaban majalisar zartarwa ta jihar wadda ta ba da amincewa.

Malam Garba ya bayyana cewa, hukumar wadda aka zabo ta a tsanake bisa la’akari da iya aiki da cancantar su, ta na da Sheikh Ibrahim Shehu Maihula a matsayin shugaba.

Kwamishinan ya kara da cewa, sauran mambobin hukumar sun hada da Ustaz Muhammad Haroun Ibn Sina, babban darakta na hukumar Hisbah; Wakilin Majalisar Masarautar Kano, Daraktan Ma’aikatan Jiha, ‘Yan sanda da Hukumar Tsaro ta Civil Defence, Hukumar Shige da Fice ta Kasa, Wakilan Ma’aikatar Shari’a ta Jiha, Ofishin Majalisar Zartaswa, da dai sauransu.

Ya kuma bayyana cewa, an kuma amince da nadin Alhaji Abdullahi Balarabe, wanda ya yi murabus sakataren dindindin a babban daraktan ma’aikatan gwamnati na jiha.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp