Gwamna jihar Kano, Dr. Abdullahi Ganduje, ya kaddamar da aikin shimfida ginin gidaje 500 a Rafin Mallam da Yola a karamar hukumar Ungogo.
Gwamna Ganduje wanda mataimakinsa Dr Nasiru Gawuna ya wakilta ya ce, aikin zai taimaka wajen rage gibin gidaje a jihar.
Ya ce gidaje 500 ne za su kasance kashi na farko, inda ya ce, za a gina rukunin gidaje 3,500 ne a yankin Tsararrun Malamai (TRA).
A cewarsa, wannan wani bangare ne na kokarin gwamnatinsa na samar da gidaje masu sauki ga ‘yan kasa, tare da tallafin gwamnatin tarayya.