Gwamnatin jihar Kano ta janye dokar takaita zirga-zirga a jihar.
Kwamishinan ‘yansandan jihar CP Salman Dogo Garba ne ya sanar da hakan a yayin zantawar sa da manema labarai a fadar gwamnatin Kano, jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar tsaron jihar da Gwamnan Jihar Abba Kabir Yusif ya jagoranta.
CP Dogo ya ƙara da cewa Gwamnatin Kano ta bada damar ne domin al’ummar su ci-gaba da fita harkokin su na yau da kullum.
A ƙarshe sanarwar tayi fatan al’umma zasu bi wannan doka domin tabbatar da zaman lafiya a lungu da saƙo dama ƙaruwar ci-gaban jihar.
Gwamnatin jihar Kano dai ta sanya dokar hana fitar ne da yammacin ranar Alhamis ɗin da ta gabata, bayan zanga-zangar matsin rayuwa ta rikiɗe zuwa fasa shagunan ‘yan Kasuwa da kuma kayan Gwamnatin ana ɗebe kayayyaki.