fidelitybank

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Date:

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da haramta bukukuwan Kauyawa da ake yi a faɗin jihar, a wani mataki na ƙarfafa kyawawan ɗabi’u tsakanin al’umma da kuma bin doka.

Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da matakin yayin wani taron manema labarai a yau Asabar, inda ya ce an kuma dakatar da dukkan wuraren gudanar da bukukuwan wato ‘event centers’ har sai abin da hali ya yi.

El-Mustapha ya ce wannan mataki da suka ɗauka wani ɓangare ne da hukumar ke yi na ƙarfafa ɗabi’u masu kyau tsakanin al’umma.

“Wannan mataki da muka ɗauka yana cikin tsarin dokar hukumar mu wanda majalisar jiha ta yi wa garambawul da kuma gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya wa hannu,” in ji El-Mustapha.

Ya ƙara da cewa dokokin sun bai wa hukumar tace finai-finai ta jihar Kano damar kula da kuma sa ido kan ayyukan da DJ (waɗanda ke saka waƙoƙi a bukukuwa) ke yi da kuma dukkan wuraren bukukuwa a faɗin jihar Kano.

“Daga yau duk wanda ya shirya biki da sunan ranar Ƙauyawa ya aikata laifi,” in ji El-Mustapha.

Ya kuma yi kira ga shugabannin al’umma da jami’an tsaro, ciki har da Hisbah da ƴan bijilanti da su haɗa-kai da hukumar domin tabbatar da cewa an bi wannan mataki na haramta bukukuwan ƙauyawa sau da kafa.

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp