fidelitybank

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa da ke siyarwa ko sayen kayan gwamnati da aka sace, musamman ƙarafunan fitilun titi, wayoyin lantarki da sauran kayayyakin da aka tanadar a tituna.

Wannan na cikin sanarwar da Khamis Bashir Bako Ayagi, mai ɗauko wa gwamna rahoto a Ma’aikatar Ayyuka ta Jihar Kano, ya fitar a ranar Litinin, 25 ga Agusta, 2025 a Kano.

Sanarwar ta ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umarci ma’aikatar ayyuka ta tattaunawa da shugabannin masu sana’ar saye da sarrafa ƙarafa a jihar.
Haka kuma an kafa kwamitin da ya ƙunshi jami’an tsaro da sauran hukumomi domin dakile wannan matsala.

Gwamnatin ta jaddada cewa duk wanda aka kama da kayan gwamnati da aka sace, ko mai siyan su daga hannun barayi, za a ɗauki matakin doka a kansa.
Sanarwar ta kuma yi kira ga iyaye, shugabannin unguwanni da masu fada a ji su ja kunnen ’ya’yansu, tare da gargadin ’yan kasuwa da su guji siyan kayayyakin da aka sace daga wuraren gwamnati.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...
X whatsapp