fidelitybank

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) kan yunƙurinta na kafa sabuwar majalisar dattawan Kano.

Gwamnatin ta bayyana cewa tun a Janairun 2024 gwamna Abba Kabir Yusuf ya kafa Majalisar Dattawan jihar ta Kano, wato (KEAC) wadda za ta riƙa ba da shawara kan ci gaban al’umma.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim Abdullahi Waiya ya fitar a yau Laraba.

Sanarwar ta ce “Tun bayan sanar da kafa wannan majalisar, ana ci gaba da shirye-shiryen da suka dace domin tabbatar da ingantaccen tsarin da zai ba da damar fara aiki yadda ya kamata.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “Wannan majalisar ba ta da wata alaƙa da siyasa ko jam’iyya, sai dai ta kasance dandalin bayar da shawara bisa hikima da gogewa.”

“Majalisar za ta ƙunshi fitattun mutane daga Kano ciki har da tsofaffin shugabanni, alƙalan kotuna, malamai, sarakuna, ƴan kasuwa da shugabannin tsaro,” kamar yadda sanarwar ta yi bayani.

Gwamnatin ta kuma bukaci dukkan ƙungiyoyi da mutane su haɗa kai da tsarin da aka kafa maimakon kirkirar wani abu sabo.

Wannan, a cewar ta, zai taimaka wajen ƙarfafa ayyukan majalisar da tabbatar da cimma burinta na kawo ci gaba da haɗin kai ga jama’ar Kano.

An ƙara da cewa nan ba da jimawa ba za a kammala tsarin kafa majalisar kafin gwamna Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da ita.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp