Dangi da ƴan’uwa gami da abokan arziƙi sun hallarci a Babban Masallacin Juma’a na Kano da sauran su, domin shaida auren zawarawa da ƴan mata da gwamnatin jihar Kano ta dauki nauyi.
Gwamnatin jihar Kano ta ce tana daukar nauyin auren zawarawa da ‘yan mata kimanin 1,500 don tallafa musu wajen gina tushen rayuwar iyali da kyautata harkokin zamantakewa.
An daura auren ne a Babban Masallacin Juma’a na Kano da wasu masallatan a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.