Ma’aikatar filaye da tsare-tsare ta kasa ta bayyana cewa a yanzu haka ta sake tantance filaye sama da 2000, tun bayan fara aikin a 2024 a matsayin wa’adin tabbatar da filaye na gwamnatin jihar Kano a ranar 31 ga Janairu, 2025.
Da yake bai wa manema labarai karin haske da safiyar Juma’a kan atisayen sake tantancewa, kwamishinan kasa da safayo da tsare-tsare na jihar, Mista Abduljabar Muhammad Umar, ya ce babu gudu babu ja da baya kan wa’adin.
Umar ya bayyana cewa, tun lokacin da aka fara tantancewar, ma’aikatar ta shaida sama da ayyuka miliyan daya na masu mallakar filaye da ke zuwa neman fom, rajista da sauran takardun tantancewa da ake bukata.
Ya yi gargadin cewa masu mallakar filaye da suka ki fitowa neman takardar shedar, suna fuskantar hadarin rasa filayensu a karshen atisayen a ranar 31 ga watan Janairu.
“Mun ba da dama don sake tantance sunayen filayen, wannan ya faru ne saboda Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi imani da yin abubuwan da suka dace da bukatun jama’ar Kano kuma an ba da wa’adin don ba kowa damar sanin aikin.”
Umar ya bayyana cewa bayan kammala atisayen tantancewa a karshen watan Janairun 2025, ma’aikatar za ta fara ba da takardar shaidar gidaje da shaguna da filayen gona, inda ta nemi masu irin wadannan kadarorin da su dauki alfanun aikin domin kayansu.
Kwamishinan filaye, ya bada tabbacin cewa daga yanzu zuwa karshen wa’adin ma’aikatan ma’aikatar za su halarci duk wanda ya zo sabunta takardar mallakar fili.