fidelitybank

Gwamnatin Kano ta bayar da wa’adin 31 ga wata kowa ya sabanta takardun filaye

Date:

Ma’aikatar filaye da tsare-tsare ta kasa ta bayyana cewa a yanzu haka ta sake tantance filaye sama da 2000, tun bayan fara aikin a 2024 a matsayin wa’adin tabbatar da filaye na gwamnatin jihar Kano a ranar 31 ga Janairu, 2025.

Da yake bai wa manema labarai karin haske da safiyar Juma’a kan atisayen sake tantancewa, kwamishinan kasa da safayo da tsare-tsare na jihar, Mista Abduljabar Muhammad Umar, ya ce babu gudu babu ja da baya kan wa’adin.

Umar ya bayyana cewa, tun lokacin da aka fara tantancewar, ma’aikatar ta shaida sama da ayyuka miliyan daya na masu mallakar filaye da ke zuwa neman fom, rajista da sauran takardun tantancewa da ake bukata.

Ya yi gargadin cewa masu mallakar filaye da suka ki fitowa neman takardar shedar, suna fuskantar hadarin rasa filayensu a karshen atisayen a ranar 31 ga watan Janairu.

“Mun ba da dama don sake tantance sunayen filayen, wannan ya faru ne saboda Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi imani da yin abubuwan da suka dace da bukatun jama’ar Kano kuma an ba da wa’adin don ba kowa damar sanin aikin.”

Umar ya bayyana cewa bayan kammala atisayen tantancewa a karshen watan Janairun 2025, ma’aikatar za ta fara ba da takardar shaidar gidaje da shaguna da filayen gona, inda ta nemi masu irin wadannan kadarorin da su dauki alfanun aikin domin kayansu.

Kwamishinan filaye, ya bada tabbacin cewa daga yanzu zuwa karshen wa’adin ma’aikatan ma’aikatar za su halarci duk wanda ya zo sabunta takardar mallakar fili.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp