fidelitybank

Gwamnatin Kano ta bayar da wa’adin 31 ga wata kowa ya sabanta takardun filaye

Date:

Ma’aikatar filaye da tsare-tsare ta kasa ta bayyana cewa a yanzu haka ta sake tantance filaye sama da 2000, tun bayan fara aikin a 2024 a matsayin wa’adin tabbatar da filaye na gwamnatin jihar Kano a ranar 31 ga Janairu, 2025.

Da yake bai wa manema labarai karin haske da safiyar Juma’a kan atisayen sake tantancewa, kwamishinan kasa da safayo da tsare-tsare na jihar, Mista Abduljabar Muhammad Umar, ya ce babu gudu babu ja da baya kan wa’adin.

Umar ya bayyana cewa, tun lokacin da aka fara tantancewar, ma’aikatar ta shaida sama da ayyuka miliyan daya na masu mallakar filaye da ke zuwa neman fom, rajista da sauran takardun tantancewa da ake bukata.

Ya yi gargadin cewa masu mallakar filaye da suka ki fitowa neman takardar shedar, suna fuskantar hadarin rasa filayensu a karshen atisayen a ranar 31 ga watan Janairu.

“Mun ba da dama don sake tantance sunayen filayen, wannan ya faru ne saboda Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi imani da yin abubuwan da suka dace da bukatun jama’ar Kano kuma an ba da wa’adin don ba kowa damar sanin aikin.”

Umar ya bayyana cewa bayan kammala atisayen tantancewa a karshen watan Janairun 2025, ma’aikatar za ta fara ba da takardar shaidar gidaje da shaguna da filayen gona, inda ta nemi masu irin wadannan kadarorin da su dauki alfanun aikin domin kayansu.

Kwamishinan filaye, ya bada tabbacin cewa daga yanzu zuwa karshen wa’adin ma’aikatan ma’aikatar za su halarci duk wanda ya zo sabunta takardar mallakar fili.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...
X whatsapp