Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ayyana ranar Laraba 4 ga Oktoba, 2023 a matsayin ranar hutu, domin tunawa da haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
Gwamnan ya bukaci al’ummar jihar da su yi amfani da lokutan bukukuwa domin yin tunani a kan koyarwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da sanya su cikin harkokinsu na yau da kullum.
Ya kuma bukaci jama’a da su rika yin addu’a da addu’o’in samun zaman lafiya da ci gaba a Kano da Najeriya baki daya.
Ya yi addu’ar Allah ya ganar damu wannan lokaci mai wuya, ya kuma sa mu dace a wannan damina da kuma damina mai zuwa. In ji Baba Halilu Dantiy, kamishinan ma’aikatar yada labarai da harkokin cikin gida a wata sanarwar da ya rabawa manema labarai.