fidelitybank

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa ta Barau FC da ta yi amfani da filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata, a matsayin filin wasa na wucin gadi a gasar cin kofin kwararru ta kasa (NPFL) na kakar 2025 da 2026.

A cewar Mataimakin Daraktan Yada Labarai na kungiyar, Ashiru Gidan Tudu, an cimma wannan matsaya ne, bayan wata ganawar sirri tsakanin wakilan Hukumar Wasanni ta Jihar Kano da shugabannin Barau FC.

Asalin filin wasa na Barau FC, shi ne filin wasa na Dambatta da ke Kano ta Arewa, yanzu haka yana kan gyare-gyare a halin yanzu domin shiryawa sabuwar kakar wasa.

Da yake jawabi a yau Talata, Shugaban Barau FC, Ibrahim Shitu Chanji, ya tabbatar da cewa, Hukumar Wasanni ta Jihar Kano ta ba da izini ga kungiyar da su yi amfani da filin wasa na Sani Abacha tsawon kakar wasar gaba daya.

“Da farko, ina so in gode wa Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabiru Yusuf, bisa amincewa da bukatar mu ta buga wasanninmu a filin wasan Sani Abacha” inji Ibrahim Shitu Chanji’.

Ya kuma yaba wa Kwamishinan Matasa da Wasanni, Mustapha Rabiu Musa Kwankwaso, bisa goyon baya da gudummawar da ya bayar.

Chanji ya kuma yi kira ga al’ummar Jihar Kano da su zama jakadu nagari tare da nuna hali na kirki a duk lokacin da suke halartar wasannin Barau FC a wannan kakar.

Barau FC zata karbi bakuncin Enyimba FC a wasan farko na gasar NPFL a ranar Lahadi, 24 ga Agusta, 2025, a filin wasan Sani Abacha, Kofar Mata, Kano.

 

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Za mu ladabtar da Jami’an mu da aka gansu suna taimakawa ‘yan siyasa a Kano – ‘Yansanda

Rundunar Æ´an sanda ta jihar Kano ta ce, ta...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baÉ—ala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...

Daga yau wankin koda a Najeriya ya koma dubu 12 maimakon dubu 50 – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya amince da rage farashin...

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...
X whatsapp