fidelitybank

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa ta Barau FC da ta yi amfani da filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata, a matsayin filin wasa na wucin gadi a gasar cin kofin kwararru ta kasa (NPFL) na kakar 2025 da 2026.

A cewar Mataimakin Daraktan Yada Labarai na kungiyar, Ashiru Gidan Tudu, an cimma wannan matsaya ne, bayan wata ganawar sirri tsakanin wakilan Hukumar Wasanni ta Jihar Kano da shugabannin Barau FC.

Asalin filin wasa na Barau FC, shi ne filin wasa na Dambatta da ke Kano ta Arewa, yanzu haka yana kan gyare-gyare a halin yanzu domin shiryawa sabuwar kakar wasa.

Da yake jawabi a yau Talata, Shugaban Barau FC, Ibrahim Shitu Chanji, ya tabbatar da cewa, Hukumar Wasanni ta Jihar Kano ta ba da izini ga kungiyar da su yi amfani da filin wasa na Sani Abacha tsawon kakar wasar gaba daya.

“Da farko, ina so in gode wa Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabiru Yusuf, bisa amincewa da bukatar mu ta buga wasanninmu a filin wasan Sani Abacha” inji Ibrahim Shitu Chanji’.

Ya kuma yaba wa Kwamishinan Matasa da Wasanni, Mustapha Rabiu Musa Kwankwaso, bisa goyon baya da gudummawar da ya bayar.

Chanji ya kuma yi kira ga al’ummar Jihar Kano da su zama jakadu nagari tare da nuna hali na kirki a duk lokacin da suke halartar wasannin Barau FC a wannan kakar.

Barau FC zata karbi bakuncin Enyimba FC a wasan farko na gasar NPFL a ranar Lahadi, 24 ga Agusta, 2025, a filin wasan Sani Abacha, Kofar Mata, Kano.

 

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp