fidelitybank

Gwamnatin Kano ki duƙufa wajen sakawa mata aikin yi – NDE

Date:

Hukumar samar da aikin yi ta kasa (NDE) ta yi kira ga gwamnatin Kano da ta tallafawa mata a kokarinta na duba matsalar rashin aikin yi, musamman a tsakanin matasa da ke addabar jihar.

Ko’odinetan hukumar ta NDE na jiha, Inuwa Abdullahi Adamu ne ya yi wannan rokon a wajen bude taron koyar da kasuwanci na kwanaki 4 (BBT), a Kano.

Adamu ya ce, duk da cewa hukumar na da kyakkyawar alaka da gwamnatin jihar Kano, amma ana bukatar karin taimako daga gare ta domin magance matsalar rashin aikin yi.

Kodinetan ya bayyana cewa, manufar BBT ita ce karfafa wa masu cin gajiyar kwarin gwiwar shiga kananan sana’o’i.

Ya ce, mahalarta 30 da aka zabo daga kananan hukumomi 8 ne za su ci gajiyar shirin, wanda wani bangare ne na shirin bunkasa harkokin kasuwanci (EDS) da NDE ta bullo da shi don sanya matasa su dogara da kansu da kuma inganta zamantakewarsu.

“Muna da wani sashen da muke kira Small Scale Enterprise Department. Mun gudanar da tsare-tsare sama da 6 a wannan sashin, inda muka horar da matasa 308 marasa aikin yi. Muna da Sashen Sana’a wanda muka gudanar da tsare-tsare guda 6. A karkashin wannan tsari, mun horar da matasa 1998 marasa aikin yi.

“Muna kuma da Sashen inganta ayyukan yi a karkara. Mun gudanar da tsare-tsare guda 4 a karkashin wannan sashe mun horar da matasa 250 marasa aikin yi.

A nasa jawabin babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kano kan harkokin kasuwanci da shiga tsakani, Baba Abdullahi ya yi alkawarin fadada adadin mahalarta taron a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp