Hukumar samar da aikin yi ta kasa (NDE) ta yi kira ga gwamnatin Kano da ta tallafawa mata a kokarinta na duba matsalar rashin aikin yi, musamman a tsakanin matasa da ke addabar jihar.
Ko’odinetan hukumar ta NDE na jiha, Inuwa Abdullahi Adamu ne ya yi wannan rokon a wajen bude taron koyar da kasuwanci na kwanaki 4 (BBT), a Kano.
Adamu ya ce, duk da cewa hukumar na da kyakkyawar alaka da gwamnatin jihar Kano, amma ana bukatar karin taimako daga gare ta domin magance matsalar rashin aikin yi.
Kodinetan ya bayyana cewa, manufar BBT ita ce karfafa wa masu cin gajiyar kwarin gwiwar shiga kananan sana’o’i.
Ya ce, mahalarta 30 da aka zabo daga kananan hukumomi 8 ne za su ci gajiyar shirin, wanda wani bangare ne na shirin bunkasa harkokin kasuwanci (EDS) da NDE ta bullo da shi don sanya matasa su dogara da kansu da kuma inganta zamantakewarsu.
“Muna da wani sashen da muke kira Small Scale Enterprise Department. Mun gudanar da tsare-tsare sama da 6 a wannan sashin, inda muka horar da matasa 308 marasa aikin yi. Muna da Sashen Sana’a wanda muka gudanar da tsare-tsare guda 6. A karkashin wannan tsari, mun horar da matasa 1998 marasa aikin yi.
“Muna kuma da Sashen inganta ayyukan yi a karkara. Mun gudanar da tsare-tsare guda 4 a karkashin wannan sashe mun horar da matasa 250 marasa aikin yi.
A nasa jawabin babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kano kan harkokin kasuwanci da shiga tsakani, Baba Abdullahi ya yi alkawarin fadada adadin mahalarta taron a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.