Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya sake buɗe kasuwar Birnin Gwari bayan kusan shekara goma tana rufe, sannan ya karɓi wasu tubabbun ƴanbindiga da suka ajiye makami suka rungumi zaman lafiya.
Ya ce gwamnatin jihar Kaduna tare da haɗin gwiwar wasu ɓangarorin gwamnatin tarayya, ta kafa kwamitin wanzar da zaman lafiya ta hanyar tattaunawa, domin samar da zaman lafiya mai ɗaurewa.
“Ta hanyar tattaunawa, yanzu mun samu amincewar mutanenmu. Yanzu manyan jagororin ƴanbindiga da dama sun miƙa wuya tare da yaransu,” in ji shi, kamar yadda shafin intanet na tashar Chanells ya ruwaito.
Ya ƙara da cewa waɗanda suka miƙa wuya, ana sanya su a shiri na musamman na gyara tunani domin tabbatar da cewa sun koma cikin al’umma sun cigaba da rayuwarsu yadda ya kamata.
Sai dai ya ce waɗanda suka ƙi miƙa wuya kuma, “ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar mataki a kan su. Tuni jami’an tsaro sun fara samun nasara a kan ƴanbindigar tare da ceto wasu waɗanda aka yi garkuwa da su,” in ji shi.