fidelitybank

Gwamnatin Kaduna ta sake bude kasuwar Birnin Gwari tun bayan shekaru 10

Date:

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya sake buɗe kasuwar Birnin Gwari bayan kusan shekara goma tana rufe, sannan ya karɓi wasu tubabbun ƴanbindiga da suka ajiye makami suka rungumi zaman lafiya.

Ya ce gwamnatin jihar Kaduna tare da haɗin gwiwar wasu ɓangarorin gwamnatin tarayya, ta kafa kwamitin wanzar da zaman lafiya ta hanyar tattaunawa, domin samar da zaman lafiya mai ɗaurewa.

“Ta hanyar tattaunawa, yanzu mun samu amincewar mutanenmu. Yanzu manyan jagororin ƴanbindiga da dama sun miƙa wuya tare da yaransu,” in ji shi, kamar yadda shafin intanet na tashar Chanells ya ruwaito.

Ya ƙara da cewa waɗanda suka miƙa wuya, ana sanya su a shiri na musamman na gyara tunani domin tabbatar da cewa sun koma cikin al’umma sun cigaba da rayuwarsu yadda ya kamata.

Sai dai ya ce waɗanda suka ƙi miƙa wuya kuma, “ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar mataki a kan su. Tuni jami’an tsaro sun fara samun nasara a kan ƴanbindigar tare da ceto wasu waɗanda aka yi garkuwa da su,” in ji shi.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp