fidelitybank

Gwamnatin Kaduna ta gargaɗi mazauna jihar su ƙauracewa gidajen su saboda ambaliya

Date:

Hukumar Bayar da agajin gaggawa ta jihar Kaduna (KADSEMA), ta yi gargaɗin mutanen da ke zama kusa da wuraren da za a iya fuskantar ambaliya da su tashi zuwa wurare marasa haɗari.

Wata sanarwa da babban sakataren hukumar Usman Mazadu ya fitar, ya ce kananan hukumomi bakwai na cikin haɗarin fuskantar ambaliya musamman ma al’ummomin da ke kusa da magudanan ruwa.

Hukumar ta bayyana cewa ya zama wajibi ta sanarwa al’ummomi yiwuwar samun ambaliyar sakamakon mamakon ruwan sama da aka samu a ranar Lahadi 19 ga watan Agusta da kuma Litinin 19 ga watan, wanda kuma ake ci gaba da tafkawa.

Ya ce mamakon ruwan sama da ake samu zai iya janyo tumbatsar koguna, musamman ma a wasu ƙananan hukumomi da ke kusa da su.

“Ya kamata waɗannan al’ummomi da ke cikin barazanar fuskantar ambaliya su kasance cikin shirin ko-ta-kwana sannan su tashi zuwa wurare marasa haɗari domin kare kansu,” in ji shi.

KADSEMA ta ce ƙananan hukumomi da ke cikin barazanar fuskantar ambaliyar sun haɗa da Kaduna ta Arewa, Kaduna ta Kudu, karamar hukumar Chikun, karamar hukumar Igabi, Sanga, Kagarko da kuma karamar hukumar Jema’a.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp