fidelitybank

Gwamnatin Kaduna ta gargaɗi mazauna jihar su ƙauracewa gidajen su saboda ambaliya

Date:

Hukumar Bayar da agajin gaggawa ta jihar Kaduna (KADSEMA), ta yi gargaɗin mutanen da ke zama kusa da wuraren da za a iya fuskantar ambaliya da su tashi zuwa wurare marasa haɗari.

Wata sanarwa da babban sakataren hukumar Usman Mazadu ya fitar, ya ce kananan hukumomi bakwai na cikin haɗarin fuskantar ambaliya musamman ma al’ummomin da ke kusa da magudanan ruwa.

Hukumar ta bayyana cewa ya zama wajibi ta sanarwa al’ummomi yiwuwar samun ambaliyar sakamakon mamakon ruwan sama da aka samu a ranar Lahadi 19 ga watan Agusta da kuma Litinin 19 ga watan, wanda kuma ake ci gaba da tafkawa.

Ya ce mamakon ruwan sama da ake samu zai iya janyo tumbatsar koguna, musamman ma a wasu ƙananan hukumomi da ke kusa da su.

“Ya kamata waɗannan al’ummomi da ke cikin barazanar fuskantar ambaliya su kasance cikin shirin ko-ta-kwana sannan su tashi zuwa wurare marasa haɗari domin kare kansu,” in ji shi.

KADSEMA ta ce ƙananan hukumomi da ke cikin barazanar fuskantar ambaliyar sun haɗa da Kaduna ta Arewa, Kaduna ta Kudu, karamar hukumar Chikun, karamar hukumar Igabi, Sanga, Kagarko da kuma karamar hukumar Jema’a.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp