fidelitybank

Gwamnatin jihar mu ta yi watsi da mu a Cyprus – Ɗaliban Zamfara

Date:

Wasu ɗaliban Najeriya ƴan asalin jihar Zamfara waɗanda ke karatu a fannoni daban-daban a Cyprus, sun koka da yadda suka ce gwamnatin jihar ta watsar da su ba tare da biyan kuɗaɗen karatun su ba.

Ɗaliban sun shaidawa BBC cewa yanzu haka basu san matsayar karatun su ba, saboda makarantarsu ta gaji da jiran a biya masu kuɗin karatu daga ɓangaren gwamnati har sun dakatar da su, lamarin da ya jefa da dama a cikin su cikin mawuyacin halin rayuwa.

Daliban dai musamman mata, da wasun su suka shafe shekaru a ƙasar, sun bayyana halin talauci da rashin damar zuwa asibiti baya ga tsangwama da suke fuskanta, tsawon shekaru, abinda hakan ke barazanar jefa wasun su aikata ba daidai ba.

Sun ce yanzu haka suna fuskantar barazanar kora daga ƙasar saboda takardunsu na neman izinin tafiya sun lallace kuma babu halin yin wasu.

Ɗaya daga cikin ɗaliban ya shaidawa BBC cewa ‘‘Tun a lokacin tsohon gwamna, Dr Bello Matawalle aka buɗe scholarship muka ciika, aka dauke mu, aka kawo mu karatu a ƙasar Cyprus mu 93, to wahalolinrayuwa ya sa mun dawo mu 88.

‘‘An bin gwamnati bashin kuɗin karatunmu, hukumar makaranta ta yi haƙuri har ta gaji. Sannan idan ka dawo maganar kudin abinci, tun 2022 gwamnatin Zamfara ba ta ƙara bamu kuɗin abinci ba.’’

Galibin daliban, da ke karatun fannonin ilmin hada magungunna, da na ɓangaren makamashi da sauran su, sun ce an raba su da iyayensu shekara biyar kenan, ga kuma rashin sanin tabbas game da makomar karatunsu, a cewar wannan dalibar.

‘‘Haka muke zaune, iyayenmu suke ƙoƙarin taimaka mana ɓangaren kuɗin abinci, musamman mu mata, duk da dai ba wani ƙarfi iyayen namu ke da shi ba, amma suna ƙoƙari su turo mana abinda za mu siya abinci.

‘‘Mun bi duk hanyoyin da ya kamata mu bi amma har yanzu abubuwa ba su daidaita ba. Mun yi missing semesters guda biyu, sheekara guda kenan, ga ita ma wagga semester har an yi nisa . ka ga idan bamu yi ta ba, shekara biyu kenan’’

Ɗalibar ta ƙara da cewa saboda tsananin fargaba da suke ciki ‘‘Ko rashin lafiya mutum ya ke yi ba ya iya zuwa asibiti. Kusan shekara biyar kenan tun da muka baro gida ba mu je ba, ka ga itama wata babbar damuwa ce a gare mu’’

BBC ta tuntuɓi gwamnatin jihar Zamfara a kan wannan batu, inda Malam Sulaiman Bala Idris mai magana da yawun gwamnan jihar, ya ce su na sane da halin da ɗaliban ke ciki, kuma matsala ce da suka gada, amma yanzu haka suna kokarin daukar matakan gaggawa domin taimakawa ɗaliban.

‘‘Matsala ce wadda ta samo asali tun daga gwamnatin da ta gabace mu, matsaloli ne marasa daɗi kuma marasa kyau. Tun kafin mu zo gwamnati ta yi watsi da su.’’ Inji Malam Sulaiman Bala Idris.

Mai magana da yawun gwamnan ya kuma ƙara da cewa ‘‘Cikin ƴan kwanakin nan, gwamnatin Zamfara za ta kai masu ɗauki, kuma za ta biya duk kuɗaɗen da ake neman’’

A lokacin gwamnatin Bello Muhammad Matawalle ne aka tura daliban domin karo ilmi, abinda jama’a ke zargin tamkar wannan gwamnati ta bar su ne cikin wannan yanayi saboda siyasa.

A Najeriya dai an sha samun gwamnatoci da ke tura dalibai a kasashen waje da sunan karatu amma daga bisani idan an samu sauyin gwamnati a watsar da su ba tare da la’akari da muhimmancin abinda za su karanta ba.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp