Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da kashe naira biliyan 1, domin samun kashi 10 cikin 100 na hannun jari a kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano (KEDCO).
Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu Sagir Musa ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron majalisar zartarwar jihar. Ya bayyana cewa za a yi amfani da kudaden ne wajen siyan hannun jari 500,000 daga Future Energy Africa Limited, babban mai saka hannun jari na KEDCO, ta yadda za a kara mallakar jihar daga kashi 7.5 zuwa kashi 10 cikin dari.
A cewar Musa, zuba jarin ya yi daidai da yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin gwamnatin jihar da KEDCO da nufin inganta wutar lantarki a fadin jihar Jigawa.
“MoU ta mayar da hankali ne kan tabbatar da samar da wutar lantarki mai inganci ga biranen Tier 1 da kuma cimma nasarar samar da wutar lantarki a yankunan karkara a fadin jihar nan da shekarar 2028,” in ji shi.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da kwangilar samar da fitulun hasken rana na Naira miliyan 595 a yankunan karkara.
Za a gudanar da aikin ne a karkashin kulawar ma’aikatar wutar lantarki da makamashi.