fidelitybank

Gwamnatin Jigawa za ta sayi hannun jari a KEDCO

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da kashe naira biliyan 1, domin samun kashi 10 cikin 100 na hannun jari a kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano (KEDCO).

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu Sagir Musa ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron majalisar zartarwar jihar. Ya bayyana cewa za a yi amfani da kudaden ne wajen siyan hannun jari 500,000 daga Future Energy Africa Limited, babban mai saka hannun jari na KEDCO, ta yadda za a kara mallakar jihar daga kashi 7.5 zuwa kashi 10 cikin dari.

A cewar Musa, zuba jarin ya yi daidai da yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin gwamnatin jihar da KEDCO da nufin inganta wutar lantarki a fadin jihar Jigawa.

“MoU ta mayar da hankali ne kan tabbatar da samar da wutar lantarki mai inganci ga biranen Tier 1 da kuma cimma nasarar samar da wutar lantarki a yankunan karkara a fadin jihar nan da shekarar 2028,” in ji shi.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da kwangilar samar da fitulun hasken rana na Naira miliyan 595 a yankunan karkara.

Za a gudanar da aikin ne a karkashin kulawar ma’aikatar wutar lantarki da makamashi.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp