fidelitybank

Gwamnatin Jigawa za ta sayi hannun jari a KEDCO

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da kashe naira biliyan 1, domin samun kashi 10 cikin 100 na hannun jari a kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano (KEDCO).

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu Sagir Musa ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron majalisar zartarwar jihar. Ya bayyana cewa za a yi amfani da kudaden ne wajen siyan hannun jari 500,000 daga Future Energy Africa Limited, babban mai saka hannun jari na KEDCO, ta yadda za a kara mallakar jihar daga kashi 7.5 zuwa kashi 10 cikin dari.

A cewar Musa, zuba jarin ya yi daidai da yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin gwamnatin jihar da KEDCO da nufin inganta wutar lantarki a fadin jihar Jigawa.

“MoU ta mayar da hankali ne kan tabbatar da samar da wutar lantarki mai inganci ga biranen Tier 1 da kuma cimma nasarar samar da wutar lantarki a yankunan karkara a fadin jihar nan da shekarar 2028,” in ji shi.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da kwangilar samar da fitulun hasken rana na Naira miliyan 595 a yankunan karkara.

Za a gudanar da aikin ne a karkashin kulawar ma’aikatar wutar lantarki da makamashi.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp