fidelitybank

Gwamnatin Jigawa ta kwakulo ma’aikatan bogi 6,348

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta gano ma’aikatan bogi 6,348 yayin binciken tantance ma’aikata da aka gudanar a jihar.

Kwamishinan Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu, Malam Sagir Musa, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Dutse.

Ya ce rahoton binciken ma’aikata na jiha da kuma rajistar tantance bayanan su ya nuna an gano ma’aikata 6,348 na bogi,

Musa ya bayyana cewa Majalisar Zartarwar Jihar ta duba rahoton sannan ta amince da kafa Cibiyar cigaba da Rijista (CCC) a ofishin Shugaban Ma’aikata na Jiha.

“Wannan matakin zai hanzarta kammala rijista da tantance ma’aikata a karkashin tsarin Integrated Payroll and Personnel Management System (IPPMS),” inji shi.

Musa ya ce aikin ya ragewa gwamanti kashe kudi da kimanin N314,657,342.06 a kowane wata da kuma N3,775,888,809.72 a shekara.

Har ila yau, kwamishinan ya ce majalisar ta amince da kwangilar gyaran hanyoyin da ambaliyar ruwa ta lalata, wanda ya hada da hanyoyin Andaza – Gadewa – Aujara; Unguwar Mani – Korayel – Rorau da Tsamiya – Yalwan Damai – Litinin Tudu a kananan hukumomin Roni, Gwiwa, da Birnin Kudu.

Sannan majalisar ta amince da kashe N254.8 miliyan don kammala shigar da al’ummomi cikin tsarin Rijistar jinkai na Jiha.

“Wannan matakin ya yi daidai da kokarin gwamnatin Umar Namadi na fadada tsarin walwala zuwa al’ummomin da ba su cikin rijistar walwala,” inji Musa.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da aiwatar da shawarwarin kwamitin kwato filayen noma da aka rarraba a fadin jihar.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp