fidelitybank

Gwamnatin Jigawa ta kwakulo ma’aikatan bogi 6,348

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta gano ma’aikatan bogi 6,348 yayin binciken tantance ma’aikata da aka gudanar a jihar.

Kwamishinan Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu, Malam Sagir Musa, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Dutse.

Ya ce rahoton binciken ma’aikata na jiha da kuma rajistar tantance bayanan su ya nuna an gano ma’aikata 6,348 na bogi,

Musa ya bayyana cewa Majalisar Zartarwar Jihar ta duba rahoton sannan ta amince da kafa Cibiyar cigaba da Rijista (CCC) a ofishin Shugaban Ma’aikata na Jiha.

“Wannan matakin zai hanzarta kammala rijista da tantance ma’aikata a karkashin tsarin Integrated Payroll and Personnel Management System (IPPMS),” inji shi.

Musa ya ce aikin ya ragewa gwamanti kashe kudi da kimanin N314,657,342.06 a kowane wata da kuma N3,775,888,809.72 a shekara.

Har ila yau, kwamishinan ya ce majalisar ta amince da kwangilar gyaran hanyoyin da ambaliyar ruwa ta lalata, wanda ya hada da hanyoyin Andaza – Gadewa – Aujara; Unguwar Mani – Korayel – Rorau da Tsamiya – Yalwan Damai – Litinin Tudu a kananan hukumomin Roni, Gwiwa, da Birnin Kudu.

Sannan majalisar ta amince da kashe N254.8 miliyan don kammala shigar da al’ummomi cikin tsarin Rijistar jinkai na Jiha.

“Wannan matakin ya yi daidai da kokarin gwamnatin Umar Namadi na fadada tsarin walwala zuwa al’ummomin da ba su cikin rijistar walwala,” inji Musa.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da aiwatar da shawarwarin kwamitin kwato filayen noma da aka rarraba a fadin jihar.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp