fidelitybank

Gwamnatin Jigawa ta kaddamar da samar da ruwan sha a jihar

Date:

An ƙaddamar da aikin samar da ruwa na Greater Dutse Water Supply a birnin Dutse na jihar Jigawa, wanda ya kusa shekara 20 ana hanƙoro domin samar da ruwan sha ga mutanen yankin.

Gwamnan jihar, Umar Namadi ne tare da ministan albarkatun ruwa da tsabtace muhalli, Farfesa Joseph Terlumun Utsev suka jagoranci ƙaddamar da aikin a garin Sintilmawa da ke ƙaramar hukumar Ringim.

An kasafta kashe naira biliyan 59.9 na aikin, wanda za a yi haɗaka tsakanin gwanmatin tarayya da jiha domin ɗaukar nauyi.

Da yake jawabi a waje ƙaddamar da shirin, gwamna Namadi ya yi godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu bisa cika alƙawarin da ya ɗauka na fara aikin.

A nasa ɓangaren, Farfesa Joseph Terlumun Utsev, yabawa ya yi game da fara aikin, inda ya ce idan aka kammala, za a samu ragowar kamuwa da cututtuka.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp