An ƙaddamar da aikin samar da ruwa na Greater Dutse Water Supply a birnin Dutse na jihar Jigawa, wanda ya kusa shekara 20 ana hanƙoro domin samar da ruwan sha ga mutanen yankin.
Gwamnan jihar, Umar Namadi ne tare da ministan albarkatun ruwa da tsabtace muhalli, Farfesa Joseph Terlumun Utsev suka jagoranci ƙaddamar da aikin a garin Sintilmawa da ke ƙaramar hukumar Ringim.
An kasafta kashe naira biliyan 59.9 na aikin, wanda za a yi haɗaka tsakanin gwanmatin tarayya da jiha domin ɗaukar nauyi.
Da yake jawabi a waje ƙaddamar da shirin, gwamna Namadi ya yi godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu bisa cika alƙawarin da ya ɗauka na fara aikin.
A nasa ɓangaren, Farfesa Joseph Terlumun Utsev, yabawa ya yi game da fara aikin, inda ya ce idan aka kammala, za a samu ragowar kamuwa da cututtuka.