fidelitybank

Gwamnatin Jigawa ta kaddamar da rabon tallafin abinci

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta ƙaddamar da rabon tallafin kayan abinci ga mabuƙata a faɗin jihar a wani mataki na rage wa al’ummar jihar raɗadin tsadar rayuwa da ake fama da shi.

Cikin wata sanarwar da Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar, Auwal D Sankara ya wallafava ashafinsa na Facebook, ya ce an ƙaddamar da rabon kayan abincin ne don tallafa wa al’umar jihar musamman a lokacin azumin watan Ramadan.

Kayayyakin da aka raba sun haɗa da buhunan shinkafa da na masara da taliya. ”An zaɓo waɗannan kayayyakin abinci ne domin biyan buƙatun al’umarmu na abinci da kuma girmamasu a wannan lokacin azumi mai ƙaratowa”, in ji sanarwar.

Kwamishinan ya ce don tabbatar da ingancin rabon kayan masarufin, gwamnatin jihar ta bi hanyar da za a kai ɗauki ga gidaje 8,000 da ba su gaza mutum uku a kowane gida ba a kowace ƙaramar hukuma.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnan jihar, Umar A. Namadi, ya ce gwamnati za ta samar da cibiyoyi biyu a kowace mazaɓa da za a riƙa ciyar da mutane a binci a lokacin azumin, don tallafa wa al’ummar jihar musamman a wanna lokaci na matsin rayuwa.

Tun dai bayan matakin cire tallafin man fetur da shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya sanar cikin watan Mayun shekarar da ta gabata, gwamnatoci a matakai daban-daban suka sha alwashin ɓullo da matakan rage wa al’ummar raɗaɗin rayuwa da cire tallafin man ya jefa su.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp