fidelitybank

Gwamnatin Guinea ta saki tsohon shugaban kasar daga gidan yari

Date:

Gwamnatin mulkin sojan kasar Guinea ta saki tsohon shugaban kasar, Alpha Conde daga gidan yari tare da sanya shi a gidan sa karkashin kulawar jami’ai.

A ranar Litinin ne DW ta wallafa a shafinta na Facebook cewa wakilinsu a Guinea ya tabbatar da cewa an sako Conde a daren Lahadi.

A ranar 5 ga Satumba 2021, sojojin kasar sun kama CondƩ a wani juyin mulki bayan da aka yi harbe-harbe a babban birnin kasar ta Conakry.

Kwamandan runduna ta musamman, Mamady Doumbouya ya fitar da wani shiri a gidan talabijin na kasar, inda ya sanar da rusa kundin tsarin mulki da gwamnati.

An rantsar da shugaban mulkin sojan mai shekaru 41, Kanar mai shekaru 41 kuma tsohon abokin hambararren CondƩ, a wani biki da aka gudanar a fadar Mohamed V da ke babban birnin kasar, Conakry, lamarin da akasarin shugabannin kasashen yammacin Afirka suka kaurace.

Gamayyar shugabannin yankin da ke karkashin kungiyar ECOWAS, ta sanya takunkumi kan ā€˜yan majalisar mulkin soja da ā€˜yan uwansu, tare da daskarar da dukiyoyinsu da kuma sanya musu takunkumin tafiye-tafiye.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko Ę“anʙwallon...

Sunderland ta ɗauko Ę“anʙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ʙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

ʘungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

ʘungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp