Gwamnatin Jihar Gombe ta ɗauki sababbin ma’aikatan lafiya 440 da zimmar kyautata harkokin lafiya a jihar.
Wata sanarwa daga fadar gwamnatin jihar ta ce, za a tura ma’aikatan wurare daban-daban a faɗin jihar, musamman cibiyoyin lafiya a matakin farko.
Da yake taya su murna, Kwamashinan Lafiya Dr Habu Dahiru ya shawarce su da su “jajirce wajen gudanar da aikinsu saboda gwamnatin Muhammadu Inuwa na bai wa ɓangaren lafiya muhimmanci”.
Shi ma sakataren Gwamnati Dr Abdulrahman Shuaibu ya nemi ma’aikatan su nuna ƙwarewa.