fidelitybank

Gwamnatin Enugu ta bi takan kaji 30,000 yayin rusau

Date:

An shiga halin fargaba a unguwar Nike da ke jihar Enugu a kudancin Najeriya, bayan gwamnati ta fara rusa gidajen mutane don gina wani sabon birni.

Mai gonar UD da ke unguwar ta Nike, Ngozi DeDe cikin hawaye ta bayyana cewa an kashe mata dabbobin da take kiwo da suka haɗa da kifi da kaji da darajarsu ta kai naira miliyan 30.

Mazauna unguwar da dama sun koka cewa gwamnati ba ta basu wata sanarwa ba kan rushe gidajen nasu, sai kawai a ranar Talata suka ga an fara rusau.

Ngozi ta shaida wa BBC cewa ” A ranar talata sai jami’an hukumon ma’aikatar Enugu suka fado mana, suka rusa gidan kaji na, kuma ba a bani wata sanarwar yin hakan ba kafin sannan.”

A cewarta a bara gwamnatin ta bayar da takarda, amma ita an gaya mata cewa bata cikin waɗanda abin zai shafa, sai gashi an zo an rushe mini gidan kaji.”

Ngozi Dede ta ce an kashe mata kaji 30,000 da kifi tarwaɗa 1,000 a gidan kaji uku da tare da lalata mata gidan ma’aikata biyu.

Yayin rusau da gwamnatin ta yi ya shafi kimanin gidaje 50.

Gwamnatin jihar ta Enugu ta sanya hannu a wata takarda na gina wani sabon birni a unguwar ta Nike.

Sai dai ya zuwa lokacin rubuta wannan rahoton, gwamnatin ta Enugu bata kai ga mayar da martani ko amsa sakonnin da BBC ta tura mata game da wannan batu.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp