fidelitybank

Gwamnatin baya ta jaza mana durƙushewar ilimi – Gwamnan Zamfara

Date:

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya koka kan yadda gwamnatin da ta shude ta ki biyan kudin jarrabawar daliban da suka kammala jarrabawar kammala sakandire ta Afirka ta Yamma, WAEC da National Examination Council, NECO na tsawon shekaru uku.

Lawal ya bayyana cews hukumar jarabawar biyu na bin gwamnati zunzurutun kudi har Naira biliyan 3.4 wanda ya ce ya jawo durkushewar fannin ilimi gaba daya a jihar.

Gwamna Lawal wanda ya yi magana ta bakin kwamishinan yada labarai da al’adu na jihar, Hon. Mannir Mu’azu Haidara, ya bayyana cewa gwamnatin da ta shude ta na bin WAEC bashin Naira biliyan 1.8, yayin da ta ci NECO biliyan 1.6.

“Daliban da suka kammala karatunsu na sakandare ba su iya ci gaba da karatunsu ba saboda WAEC da NECO sun ki fitar da sakamakonsu na tsawon shekaru uku.

“Amma lokacin da gwamnati mai ci ta zo, ta kawar da basussukan tare da tabbatar wa hukumar jarrabawar biyan kudi cikin gaggawa,” inji shi.

Da yake jawabi, ya bayyana cewa gwamnatin Dauda Lawal ta sake bude hukumar ciyar da makarantun jihar da aka rufe saboda ba za ta iya biyan ‘yan kwangilar da ke kai wa daliban kayan abinci ba.

A cewarsa, gwamnati mai ci ta gaji rugujewar tsarin mulki ne sakamakon durkushewar bangarorin ilimi, tsaro, tattalin arziki da dai sauransu.

A ci gaba da cewa, Haidara ya jaddada cewa, a lokacin da sabuwar gwamnati ta hau mulki, ta gaji ma’aikata da ‘yan fansho da ke bin bashin albashin watanni hudu, wanda ya ce gwamnatin Lawal ta wanke.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp