fidelitybank

Gwamnatin APC ba ta damu da rayuwar ‘yan Najeriya ba – PDP

Date:

Jam’iyyar PDP a Najeriya ta zargi jam’iyyar APC mai mulkin kasar da nuna halin ko-in-kula game da matsalar tsaro da ta addabi kasar, lamarin da ta ce shi ne ya janwo mummunan harin da wasu ‘yan bindiga suka kai kan jirgin kasan da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna, abin da ya yi sanadin mutuwar akalla mutum takwas da jikkatar mutane da dama.

A wata sanarwa da ta fitar dauke da sa hannun sakataren yada labaranta na kasa, Debo Ologunagba, jami’iyar ta PDP ta yi kakkausar suka kan abin da ta kira rikon-sakinar-kashin da gwamnatin APC ke yi wa harkar tsaro a kasar.

Babbar jam’iyyar adawar dai na shan zargin gwamnatin APC da gazawa, amma kuma galibi ta fi yin matsin lamba kan batun matsalar tsaron wacce ta bayyana ta rinjaye sauran matsalolin da ake fama da su a kasar.

Ta ce kalaman da Ministan Sufuri Rotimi Amaechi da kuma gwamnan jihar Kaduna Nasiru El-Rufai suka yi game da matsalolin tsaron da cewa hakan ya tabbatar da cewa akwai hadin-baki tsakanin ‘yan ta’adda da gwamnatin APC.

“Ikirarin da gwamnan Kaduna Malam el-Rufai da kuma Ministan Sufuri Rotimi Amaechi suka yi game da batun hare-haren ‘yan bindigar ya tabbatar da zargin da jam’iyar PDP ke yi cewa gwamnatin APC ta san inda ‘yan ta’addar suke, kana ta san shirin da suke yi na tayar da zaune tsaye a kasar amma ta ki daukar matakai da gangan,” in ji sanarwar.

”Ministan Sufuri Rotimi Amaechi ya ce wasu ministocin APC mai mulki sun yi kafar-angulu wa bukatun da ya gabatar a taron majalisar ministoci cewa a kafa na’urorin bincike don kauce wa hare-haren ta’addanci a kan titin jiragen kasa na Kaduna zuwa Abuja, ya kara tabbatar da zargin cewa gwamnatin ta APC na bai wa ‘yan ta’adda damar gudanar da ayyukan ta’addancinsu cikin sauki kasar,” a cewar PDP.

A wani jawabi da Gwamna Nasiru El- Rufai ya yi a bainar jama’a a baya bayan nan ne in ji jam’iyar ta PDP, shi da kan ya yi wa gwamnatin ta APC bankada, wanda ta ce shi ma yana ciki – ya ce: “Mun san inda sansanoninsu suke, mun san inda suke, jami’an tsaron farin-kaya na SSS na da lambobin wayarsu, suna sauraronsu kuma suna ba ni rahoto. iN JI bbc.

Kazalika PDP ta jaddada ikirarin Ministan Sufuri Ameachi inda yake cewa: “Muna sane da matsalolin da za su faru. Mun san cewa muna bukatar na’urorin zamani …. Na yi gargadin cewa za a tafka asarar rayuka kuma ga shi yanzu an rasa rayuka…A lokacin da ka tunkari gwamnati da gaskiyar niyya amma abokan aikinka suka rika taka maka birki, abin bakin-ciki ne.”

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu É—auki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta É—aukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu Æ™awayen Amurka za su É—anÉ—anar kuÉ—arsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta É—aure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miÆ™a saÆ™on ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp