Gwamnatin jihar Akwa Ibom ta sanya dokar hana fita daga maraice zuwa wayewar gari, domin dakile barkewar rikicin da ke faruwa tsakanin masuntan Yarbawa, Ilajes da ’yan asalin yankin Ibeno a jihar.
Rikicin wanda ya afku a ranar Laraba ya yi sanadiyar salwantar rayuka da dukiyoyi na miliyoyin naira.
Shugaban karamar hukumar Ibeno, Henry Mkpa, wanda ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran sa, Melford Asuquo.
Ya ce, matakin ya kasance umarni ne daga gwamnatin jihar cewa, dokar ta hana zirga-zirgar mutane da ababen hawa a cikin jihar. al’ummomin da ke cikin kogi daga karfe 7:00 na yamma zuwa karfe 6:00 na safe, tare da aiwatar da hakan nan take.