Gwamnan jihar Adamawa ta yanke shawarar hana kai Shanu yankunan Kudu, saboda toshe yoyon kudaden shiga da kuma ingantashi ta hanyar kaiwa wasu jihohi.
Sakataren gwamnatin jihar, Bashir Ahmad, ya yi bayanin wannan sabuwar dokar.
Ya ce, gwamnatin jihar ta yanke shawarar hana kai Shanu wasu jihohin Kudu cikin har da Legas, saboda suna karbar harajin Naira 35,000 kan shanu guda.
A cewarsa, hana kaiwa yankunan zai taimakawa tattalin arzikin gida.
Ya ce: “Abinda muke karba matsayin harajin Shanu bai kai abinda ake karba hannun masu kaiwa kudu ba a hanya. Mutane kan kai Shanu Legas daga Mubi, amma a hanya suna biyan N,5000 kan kowani shanu, kuma ana karba kimanin sau biyar kan su isa.” In ji Bashir.