fidelitybank

Gwamnati za ta yi gwanjan rukunin Gidajen Emefiele

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, za yi wa ƴan Najeriya gwanjon rukunin gidaje da ta ƙwace a Abuja a hannun tsohon gwamnan babban bankin ƙasar, Godwin Emefiele.

Bayanin haka ya fito ne lokacin da ministan ma’aikatar gidaje da raya birane Ahmed Dangiwa da kuma shugaban hukumar EFCC Olanipekun Olukoyede, suka jagoranci wata tawaga zuwa rukunin gidajen da aka ƙwace, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

EFCC ce ta ƙwace gidajen waɗanda ke alaƙa da Emefiele a watan Disamban 2024, inda aka miƙa su ga ma’aikatar bayan umarni da shugaba Tinubu ya bayar.

Lokacin ziyarar gani da idon, Dangiwa ya sanar da cewa ma’aikatar za ta fara aikin duba ingancin gidajen.

Ya ce bayan kammala duba su, za a samar da wani shafi wanda ƴan Najeriya za su shiga su nemi damar saya.

Ministan ya ƙara nanata zimmar gwamnatin tarayya wajen yin komai bisa gaskiya da adalci, inda ya yi kira ga jami’an gwamnati da su guji shiga abubuwan da ba su dace ba.

A watan Afrilun 2025 ne, wata babbar kotun tarayya a Abuja ta yi watsi da buƙatar tsohon gwamnan Babban Bankin na neman a dawo masa da rukunin gidajen da gwamnati ta ƙwace.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp