fidelitybank

Gwamnati za ta yi gwanjan rukunin Gidajen Emefiele

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, za yi wa ƴan Najeriya gwanjon rukunin gidaje da ta ƙwace a Abuja a hannun tsohon gwamnan babban bankin ƙasar, Godwin Emefiele.

Bayanin haka ya fito ne lokacin da ministan ma’aikatar gidaje da raya birane Ahmed Dangiwa da kuma shugaban hukumar EFCC Olanipekun Olukoyede, suka jagoranci wata tawaga zuwa rukunin gidajen da aka ƙwace, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

EFCC ce ta ƙwace gidajen waɗanda ke alaƙa da Emefiele a watan Disamban 2024, inda aka miƙa su ga ma’aikatar bayan umarni da shugaba Tinubu ya bayar.

Lokacin ziyarar gani da idon, Dangiwa ya sanar da cewa ma’aikatar za ta fara aikin duba ingancin gidajen.

Ya ce bayan kammala duba su, za a samar da wani shafi wanda ƴan Najeriya za su shiga su nemi damar saya.

Ministan ya ƙara nanata zimmar gwamnatin tarayya wajen yin komai bisa gaskiya da adalci, inda ya yi kira ga jami’an gwamnati da su guji shiga abubuwan da ba su dace ba.

A watan Afrilun 2025 ne, wata babbar kotun tarayya a Abuja ta yi watsi da buƙatar tsohon gwamnan Babban Bankin na neman a dawo masa da rukunin gidajen da gwamnati ta ƙwace.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...

Majalisar Dinkin Duniya za ta dakatar da tallafin abinci a Najeriya

Shirin Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana...

Tinubu ya na murkushe ‘Yan adawa – Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya ce...

Gwamnatin Kano ta baiwa yara fifiko – UNICEF

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya...

Majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 21

A ranar Talata ne majalisar Dattawa ta amince da...

An sallami Gwamnan Katsina daga asibiti bayan ya samu rauni a hatsarin mota

An sallami gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda,...

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...
X whatsapp