Gwamnatin tarayya ta ce, za yi wa ƴan Najeriya gwanjon rukunin gidaje da ta ƙwace a Abuja a hannun tsohon gwamnan babban bankin ƙasar, Godwin Emefiele.
Bayanin haka ya fito ne lokacin da ministan ma’aikatar gidaje da raya birane Ahmed Dangiwa da kuma shugaban hukumar EFCC Olanipekun Olukoyede, suka jagoranci wata tawaga zuwa rukunin gidajen da aka ƙwace, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.
EFCC ce ta ƙwace gidajen waɗanda ke alaƙa da Emefiele a watan Disamban 2024, inda aka miƙa su ga ma’aikatar bayan umarni da shugaba Tinubu ya bayar.
Lokacin ziyarar gani da idon, Dangiwa ya sanar da cewa ma’aikatar za ta fara aikin duba ingancin gidajen.
Ya ce bayan kammala duba su, za a samar da wani shafi wanda ƴan Najeriya za su shiga su nemi damar saya.
Ministan ya ƙara nanata zimmar gwamnatin tarayya wajen yin komai bisa gaskiya da adalci, inda ya yi kira ga jami’an gwamnati da su guji shiga abubuwan da ba su dace ba.
A watan Afrilun 2025 ne, wata babbar kotun tarayya a Abuja ta yi watsi da buƙatar tsohon gwamnan Babban Bankin na neman a dawo masa da rukunin gidajen da gwamnati ta ƙwace.