fidelitybank

Gwamnati za ta magance satar danyen man fetur a Najeriya

Date:

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da gwamnoni sun kafa kwamatoci kan satar ɗanyen mai da kuma na harkokin tattalin arziki.

An ɗauki matakin ne a taron majalisar tattalin arziki ta Najeriya karo na 138 wanda aka yi ta intanet ranar Alhamis.

A cewar sanarwar da mai taimaka wa mataimakin shugaban Najeriyar kan harkokin yaɗa labarai, Stanley Nkwocha ya fitar, kwamatocin za su kasance ƙarƙashin shugabancin gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdurrazak da takwaransa na jihar Imo, Hope Uzodinma.

Ya ce an yi taron ne bayan tattaunawar da aka yi game da matsalolin da suka shafi tattalin arziki da kuma nazari kan tsare-tsaren magance matsin tattalin arziki na gajere da dogon zango.

Kwamitin inganta tattalin arzikin yana da alhakin samar da tsarin kula da batun cire tallafin mai da bijiro da tsarin kare tattaunawar albashin ma’aikata da batun hauhawar farashin kayayyaki da sauran lamuran da suka danganci tattalin arziki.

Mambobin kwamitin sun haɗa da gwamnan jihar Gombe mai wakiltar arewa maso gabas da gwamnan Legas mai wakiltar kudu maso yamma sai gwamnan Akwa Ibom mai wakiltar kudu maso kudu da gwamnan Anambra mai wakiltar kudu masu gabas da gwamnan Neja mai wakiltar arewa ta tsakiya da gwamnan Kaduna mai wakiltar arewa maso yamma.

..

A ɗaya ɓangaren, kwamitin da aka kafa wanda zai kula da ɗanyen mai da magance satar shi zai zama a ƙarƙashin jagorancin gwamna Hope Uzodinma na jihar Imo.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da gwamnan Ogun mai wakiltar Kudu ta yamma da gwamnan Plateau mai wakiltar arewa ta tsakiya sai gwamnan Rivers mai wakiltar kudu maso kudu da gwamnan Borno mai wakiltar arewa maso gabas sai gwamnan Jigawa mai wakiltar arewa maso yamma da gwamnan Abia mai wakiltar yankin kudu maso gabas sai ministan kasafin kuɗi da tsare-tsare da ministan kuɗi da gwamnan babban bankin ƙasa sai shugaban kamfanin NNPCL da shugaban hukumar raya yankin Neja Delta, NDDC da manyan hafsoshin tsaro.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp