Shugaban hukumar lafiya matakin farko Dr Faisal Shuaib ya ce, hukumarsa za ta yi aiki da hukumar NAFDAC, domin tsayar da ranar da za a lalata allurar rigakafin Korona da ta lalace.
Hukumomin sun tabbatar da cewa suna shirin lalata allurar rigakafin korona kimanin miliyan É—aya sakamakon rashin amfani da su.
Zuwa yanzu kashi biyu ne kawai suka yi rigakafi a Najeriya mai yawan al’umma miliyan 200.
Hukumomin sun ce wa’adin aikinsu ne ya ƙare, domin haka ba su dace a yi amfani da su ba.
Wannan ne dai karon farko da hukumomin lafiya a Najeriya suka sanar da yawan rigakafin da za a lalata.