Mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo ne ya bayyana hakan a yayin wani bayani da ya yi kan rahoton ci gaban da aka samu a shirin rage talaucin na ƙasa da ake kira NPRGS a gaban kwamitin da ya jagoranta a ranar Laraba.
Ayyuakan da aka tsara aiwatarwa a bana ƙarƙashin NPRGS sun haɗa da: “Gina gidaje dubu ɗari ga masu ƙaramin ƙarfi, wanda zai samar da ayyukan yi miliyan ɗaya na kai-tsaye ko a fakaice.
“Faɗaɗa samun makamashi ta hanyar samar da fitilun gefen titi 1,200 a yankunan karkara da kuma wasu ƙananan tashoshin wuta da za a riƙa amfani da su a gonaki ƙarƙashin shirin Solar Naija.
“Samar da ayyuka miliyan huɗu da ɗari biyar na kai-tsaye ko kuma a fakaice ta hanyar shirin gina hanyoyi a yankin karkara waɗanda za su haɗa kasuwannin ƙauye 750 a faɗin Najeriya.
“Samar da taimakon naira biliyan tara ga masu gonakin da ba su da karfi a lokacin daminar bana karkashin shirin samar da akin yi a bangaren noma.
“Fadada rajistar mutanen da ke samun tallafin rayuwa da karin sunayen magidanta miliyan uku.”
A lokacin gabatar da bayanin, Ministan kasafin kudi da tsare tsare, Clem Agba, ya ce mutum miliyan biyu ne suka amfana da shirin NPRGS kai-tsaye a 2022.
Rahotansa ya bayyana cewa manoma miliyan daya da dubu 600 ne suka mafana da shirin karkashin shirin habbaka noma.
Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin shugaban Najeriyan ya fitar a jiya, ya ce matasa 13,000 sun samu horo kan kere-kere da kuma sana’o’in hannu a jihohi 6 da suka hada da Legas da Ogun da Enugu da Gombe da Kaduna da Nasarawa, yayin da ake shirin samar da irin wannan tsari ga matasa 2,000 a jihar Edo.
Ya ce sama da ‘yan Najeriya 8,000 aka ɗauka aikin shimfiɗa tituna a yankin karkara ƙarƙashin shirin samar da hanyoyi a karkara, inda aka gina hanyoyi 40 cikin kauyuka 120 a faɗin Najeriya.
“A duka Najeriya mutum 1,818,782 ne suke cin gajiyar shirin NPRGS, kuma an ɗauki mutum 9,527 aiki ƙarƙashin aikin ya zuwa yanzu.”