fidelitybank

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Date:

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da wasu kamfanoni domin gina titin jirgn ƙasa mai ɗankaren gudu da zai kai tsawon kilomita 4,000 a jihohi shida na ƙasar.

Kamfanin De-Sadel Nigeria Ltd. na Najeriya da kuma China Liancai Petroleum Investment Holdings Limited na ƙasar China ne za su yi aikin, kamar yadda ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya George Akume ya bayyana ranar Talata.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa wani kwamati ya gabatar wa Mista Akume ranar Talata bayanin kuɗaɗen kusan dala biliyan 60 da aikin zai laƙume.

A cewar shugaban kamfamnin De-Sadel Nigeria Limited, Mr Samuel Uko, matakin farko na layin dogon zai haɗe jihohin Legas da Abuja da Kano da kuma Rivers, inda zai kai nisan aƙalla kilomita 1,600.

“Aikin zai kasance mataki-mataki. Da zarar mun kammala wani mataki ‘yan Najeriya za su fara amfana da jirgin kafin cikar wata 36 da aka ɗiba domin kammala aikin baki ɗaya,” in ji Mista Uko.

Sakataren gwamnati ya ce ofishinsa zai mayar da hankali wajen tsettsefe bayanan kuɗin da za a kashe kafin gwamnatin Bola Tinubu ta bayar da umarnin fara aikin.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp