fidelitybank

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Date:

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da wasu kamfanoni domin gina titin jirgn ƙasa mai ɗankaren gudu da zai kai tsawon kilomita 4,000 a jihohi shida na ƙasar.

Kamfanin De-Sadel Nigeria Ltd. na Najeriya da kuma China Liancai Petroleum Investment Holdings Limited na ƙasar China ne za su yi aikin, kamar yadda ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya George Akume ya bayyana ranar Talata.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa wani kwamati ya gabatar wa Mista Akume ranar Talata bayanin kuɗaɗen kusan dala biliyan 60 da aikin zai laƙume.

A cewar shugaban kamfamnin De-Sadel Nigeria Limited, Mr Samuel Uko, matakin farko na layin dogon zai haɗe jihohin Legas da Abuja da Kano da kuma Rivers, inda zai kai nisan aƙalla kilomita 1,600.

“Aikin zai kasance mataki-mataki. Da zarar mun kammala wani mataki ‘yan Najeriya za su fara amfana da jirgin kafin cikar wata 36 da aka ɗiba domin kammala aikin baki ɗaya,” in ji Mista Uko.

Sakataren gwamnati ya ce ofishinsa zai mayar da hankali wajen tsettsefe bayanan kuɗin da za a kashe kafin gwamnatin Bola Tinubu ta bayar da umarnin fara aikin.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp