fidelitybank

Gwamnati za ta fara yi wa Dabbobi allurar rigakafi cutar Anthrax

Date:

Gwamnatin tarayya na shirin yi wa dabbobi huji ko riga-kafin cutar Anthrax, bayan ɓullar cutar a wata gona da ke Suleja a jihar Neja.

Ma’aikatar noma ta ce, ta ɗauki matakan da suka dace don daƙile cutar da hana yaɗuwarta, kuma gonar da ake magana, wadda ake kiwon shanu da tumaki da Awaki, har ta ɗauki matakan keɓe ta tare da sa’ido a kan ta.

Tun a watan Yunin da ya wuce, gwmanatin Najeriyar ta ankarar da al`ummar ƙasar game da ɓullar cutar a ƙasashen Ghana da Burkina Faso da kuma Togo. Wannan ne ma ya sa mahukunta suka gargaɗi al`umma da suke dinga ɗaukar matakan kariya.

Wani kwararren likitan dabbobi a Najeriya, Dakta Abubakar Sulaiman, ya ce duk da cewa cutar ba ta da saurin yaɗuwa, amma bil`adama ma kan harbu da ita idan ya ci nama ko gogayya da jikin dabbar da ta harbu.

Ya ce, ɗaya daga cikin manyan hanyoyin kariya daga cutar, ita ce yi wa dabbobi huji kamar yadda mahukunta suka yi aniya.

A ƴan makwannin da suka wuce ne aka samu labarin ɓullar cutar a ƙasashen Ghana da Burkina Faso da kuma Togo.

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp