Gwamnatin tarayya na shirin yi wa dabbobi huji ko riga-kafin cutar Anthrax, bayan ɓullar cutar a wata gona da ke Suleja a jihar Neja.
Ma’aikatar noma ta ce, ta ɗauki matakan da suka dace don daƙile cutar da hana yaɗuwarta, kuma gonar da ake magana, wadda ake kiwon shanu da tumaki da Awaki, har ta ɗauki matakan keɓe ta tare da sa’ido a kan ta.
Tun a watan Yunin da ya wuce, gwmanatin Najeriyar ta ankarar da al`ummar ƙasar game da ɓullar cutar a ƙasashen Ghana da Burkina Faso da kuma Togo. Wannan ne ma ya sa mahukunta suka gargaɗi al`umma da suke dinga ɗaukar matakan kariya.
Wani kwararren likitan dabbobi a Najeriya, Dakta Abubakar Sulaiman, ya ce duk da cewa cutar ba ta da saurin yaɗuwa, amma bil`adama ma kan harbu da ita idan ya ci nama ko gogayya da jikin dabbar da ta harbu.
Ya ce, ɗaya daga cikin manyan hanyoyin kariya daga cutar, ita ce yi wa dabbobi huji kamar yadda mahukunta suka yi aniya.
A ƴan makwannin da suka wuce ne aka samu labarin ɓullar cutar a ƙasashen Ghana da Burkina Faso da kuma Togo.