fidelitybank

Gwamnati za ta daina biyan kudin tallafin man fetur – Ministar Kudi

Date:

Ministar kuɗi, kasafi da tsare-tsare ta Najeriya Hajiya Zainab Ahmed ta ce, gwamnatin tarayya za ta daina biyan kuɗin tallafin man fetur a watan Yunin 2023.

Hajiya Zainab ta bayyana haka ne a lokacin taron manema labarai da ta gudanar a Abuja babban birnin ƙasar bayan kammala taron tattalin arziki na ƙasa karo na 28.

Kamfanin dillacin labaran ƙasar ya ruwaito cewa biyan tallafin kudin man fetur ya laƙume naira tiriliyan 2.565 tsakanin watan Janairu zuwa Agustan 2022.

Haka kuma a cikin kasafin kudinta, gwamnatin tarayya ta ƙiyasta kashe naira tiriliyan 3.3 wajen biyan tallafin man tsakanin watan Janairu zuwa Yunin 2023.

Ta ci gaba da cewa kuɗin tallafin man na kawo wa kasafin kudin giɓin da dole sai an ciwo bashi kafin cike shi.

“Ba kuɗi ne da muke da su a hannu ba, kudi ne da muke karɓo bashinsu domin biyan tallafin”, in ji ministar.

“Wasu ƙasashe sun fara biyan tallafi saboda annobar Korona, da batun yaƙin Ukraine, to amma suna amfani da kuɗaɗensu wajen biyan tallafin, to amma mu bashi muke karɓowa domin biyan tallafin, to kun ga duka biyu kenan, dan haka dole mu dakatar da shi”, in ji ministar

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...
X whatsapp