fidelitybank

Gwamnati tarayya ta miƙa cibiyar wutar ta Zungeru ga ƴan kasuwa

Date:

Gwamnatin tarayya ta miƙa ragamar harkokin cibiyar wutar lantarki na Zungeru zuwa ga wani kamfani mai zaman kansa na Penstock Limited.

An bayyana haka ne a taron farko na hukumar NCP da ke tantance kadarorin gwamnati da suka kamata a sayar a bana da aka yi a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

Ana sa rai matakin zai inganta harkar samar da wutar lantarki tare da bayar da gudummawa sosai ga biyan buƙatun ƴan ƙasa game da makamashi.

An cimma yarjejeniyar ranar 13 ga watan Disamban 2023 tsakanin hukumar kula da kadarorin gwamnati BPE da kamfanin na Penstock Limited.

Bayan amincewar hukumar NCP, kamfanin ya amince ya biya kashi hamsin cikin 100 na kuɗin soma aiki ranar 5 ga watan Janairu.

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima wanda ya jagoranci taron ya bayyana ƙudurin gwamnatin tarayya na sake fasalta bankin tallafawa ayyukan noma domin haɓaka ɓangaren noma da samar da abinci a ƙasa.

Da yake magana a taron, Shettima ya bayyana irin rawar da bankin zai taka wajen samar da abinci a ƙasa inda ya yi magana kan rassan bankin da ke yankunan Najeriya.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp