fidelitybank

Gwamnati ta zargi jam’iyyun siyasa da kawo mata tsaiko

Date:

A ranar Talata ne gwamnatin tarayya, ta zargi wasu jam’iyyun adawa da haramtawa shugaban kasa Muhammadu Buhari a bisa doka ba da taimako ga ‘yan Najeriya da ke fama da kuncin rayuwa sakamakon sake fasalin Naira.

Lai Mohammed, ministan yada labarai da al’adu, shine ya bayyana hakan a bugu na 23 na jerin gwanatin shugaban kasa Muhammadu Buhari (2015-2023) a ranar Talata.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito cewa, an shirya shirin ne domin nuna irin nasarorin da gwamnatin Buhari ta samu.

Karanta Wannan: Gwamnatin Zamfara ta magantu akan wahlar da bankuna

A jawabinsa na bude taron, Ministan ya ce Gwamnatin Tarayya ta yi la’akari da irin matsalolin da ‘yan Najeriya ke fuskanta, saboda sake fasalin kudin Naira da kuma matsalar samar da mai.

A cewarsa, gwamnati na aiki tukuru don maido da al’amuran da suka shafi tattalin arziki guda biyu.

Ya ce, abin mamaki ne yadda wasu jam’iyyun siyasa na adawa suka garzaya kotu domin samun umarnin hana Buhari da babban bankin Najeriya kara wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu ga ‘yan Nijeriya su musanya tsofaffin takardun su da sababbi.

Mohammed ya ce, “ Matakin kotun ya zo ne bayan da jam’iyyun adawa da dama suka yi barazanar kauracewa zaben 2023 idan aka kara wa’adin.

“Wadannan abubuwan ban mamaki da jam’iyyun da abin ya shafa suka nuna a sarari cewa ‘yan adawa sun mayar da wannan batun gaba daya zuwa wasan siyasa, sun gwammace su kara sanya ‘yan Najeriya wahala a kan bagadin wasan kwaikwayo na siyasa da ba a sani ba.”

Mohammed ya kara da cewa, “ko kuma ta yaya mutum zai iya bayyana gaskiyar cewa wadannan jam’iyyun adawa marasa gaskiya ba sa son wani mataki da zai iya rage radadin da ‘yan Najeriya ke ciki?.”

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaÉ—i masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga FalasÉ—inawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen É—an gwagwarmayar nan kuma É—an jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp