fidelitybank

Gwamnati ta zargi jam’iyyun siyasa da kawo mata tsaiko

Date:

A ranar Talata ne gwamnatin tarayya, ta zargi wasu jam’iyyun adawa da haramtawa shugaban kasa Muhammadu Buhari a bisa doka ba da taimako ga ‘yan Najeriya da ke fama da kuncin rayuwa sakamakon sake fasalin Naira.

Lai Mohammed, ministan yada labarai da al’adu, shine ya bayyana hakan a bugu na 23 na jerin gwanatin shugaban kasa Muhammadu Buhari (2015-2023) a ranar Talata.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito cewa, an shirya shirin ne domin nuna irin nasarorin da gwamnatin Buhari ta samu.

Karanta Wannan: Gwamnatin Zamfara ta magantu akan wahlar da bankuna

A jawabinsa na bude taron, Ministan ya ce Gwamnatin Tarayya ta yi la’akari da irin matsalolin da ‘yan Najeriya ke fuskanta, saboda sake fasalin kudin Naira da kuma matsalar samar da mai.

A cewarsa, gwamnati na aiki tukuru don maido da al’amuran da suka shafi tattalin arziki guda biyu.

Ya ce, abin mamaki ne yadda wasu jam’iyyun siyasa na adawa suka garzaya kotu domin samun umarnin hana Buhari da babban bankin Najeriya kara wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu ga ‘yan Nijeriya su musanya tsofaffin takardun su da sababbi.

Mohammed ya ce, “ Matakin kotun ya zo ne bayan da jam’iyyun adawa da dama suka yi barazanar kauracewa zaben 2023 idan aka kara wa’adin.

“Wadannan abubuwan ban mamaki da jam’iyyun da abin ya shafa suka nuna a sarari cewa ‘yan adawa sun mayar da wannan batun gaba daya zuwa wasan siyasa, sun gwammace su kara sanya ‘yan Najeriya wahala a kan bagadin wasan kwaikwayo na siyasa da ba a sani ba.”

Mohammed ya kara da cewa, “ko kuma ta yaya mutum zai iya bayyana gaskiyar cewa wadannan jam’iyyun adawa marasa gaskiya ba sa son wani mataki da zai iya rage radadin da ‘yan Najeriya ke ciki?.”

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp