A ranar Talata ne gwamnatin tarayya, ta zargi wasu jam’iyyun adawa da haramtawa shugaban kasa Muhammadu Buhari a bisa doka ba da taimako ga ‘yan Najeriya da ke fama da kuncin rayuwa sakamakon sake fasalin Naira.
Lai Mohammed, ministan yada labarai da al’adu, shine ya bayyana hakan a bugu na 23 na jerin gwanatin shugaban kasa Muhammadu Buhari (2015-2023) a ranar Talata.
Kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito cewa, an shirya shirin ne domin nuna irin nasarorin da gwamnatin Buhari ta samu.
Karanta Wannan:Â Gwamnatin Zamfara ta magantu akan wahlar da bankuna
A jawabinsa na bude taron, Ministan ya ce Gwamnatin Tarayya ta yi la’akari da irin matsalolin da ‘yan Najeriya ke fuskanta, saboda sake fasalin kudin Naira da kuma matsalar samar da mai.
A cewarsa, gwamnati na aiki tukuru don maido da al’amuran da suka shafi tattalin arziki guda biyu.
Ya ce, abin mamaki ne yadda wasu jam’iyyun siyasa na adawa suka garzaya kotu domin samun umarnin hana Buhari da babban bankin Najeriya kara wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu ga ‘yan Nijeriya su musanya tsofaffin takardun su da sababbi.
Mohammed ya ce, “ Matakin kotun ya zo ne bayan da jam’iyyun adawa da dama suka yi barazanar kauracewa zaben 2023 idan aka kara wa’adin.
“Wadannan abubuwan ban mamaki da jam’iyyun da abin ya shafa suka nuna a sarari cewa ‘yan adawa sun mayar da wannan batun gaba daya zuwa wasan siyasa, sun gwammace su kara sanya ‘yan Najeriya wahala a kan bagadin wasan kwaikwayo na siyasa da ba a sani ba.”
Mohammed ya kara da cewa, “ko kuma ta yaya mutum zai iya bayyana gaskiyar cewa wadannan jam’iyyun adawa marasa gaskiya ba sa son wani mataki da zai iya rage radadin da ‘yan Najeriya ke ciki?.”