Gwamnatin tarayya ta yi watsi da rahoton da ke cewa sojoji sun zubar wa mata ciki a asirce a jihar Borno.
Ministan yada labaran kasar Lai Mohammed ya karyata rahoton da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya fitar a makon da ya gabata wanda ya ce cikin shekara tara dubban mata ne aka zubar wa ciki a wani shiri na rundunar sojin kasar.
Rahoton ya ce, galibin matan wadanda suka samu juna biyu ne tare da mayakan Boko Haram.
Reuters ya ce ya tattauna da mata da ‘yan mata da dama wadanda suka bayyana yadda aka yi ba su magani da yi masu allura – kafin daga baya suka fahimci na zubar da ciki ne.