Iyalan Taiwo Michael Akinkunmi, mutumin da ya zana tutar Najeriya, sun ce sun gaji da jiran jana’izar karramawar da aka yi musu alƙawari, shekara guda bayan rasuwarsa yana da shekaru 87.
A maimokon jiran jana’izar da aka yi musu alƙwari, iyalan sun ce za su binne Akinkunmi, wanda aka fi sani da “Mr. Flag” a wannan makon a jihar Oyo, inda ya ke zauna.
Duk da fatan jana’izar da jihar ta yi, ɗan Akinkunmi, Akinwumi Akinkunmi, ya bayyana cewa iyalan sun zaɓi su binne shi, tare da tallafin da gwamnatin jihar Oyo ta bayar.
“Dole ne mu yi masa jana’izar da ya dace,” Akinwumi ya shaida wa BBC Focus on Africa podcast.
Taiwo Akinkunmi, wanda ya zana tutar Najeriya kafin ƙasar ta samu ‘yancin kai a 1960, mutum ne mai tawali’u.
An haife shi ne a Jihar Ibadan kuma ya yi aiki a matsayin ma’aikacin gwamnati a ma’aikatar noma har zuwa lokacin da ya yi ritaya a shekarar 1994.
Duk da irin gudunmawar da Akinkunmi ya bayar, har zuwa lokacin da Nijeriya ta cika shekaru 50 da samun ‘yancin kai, ba a san shi ba a matsayin ɗaya daga cikin fitattun ‘yan Nijeriya 50.
Bayan rasuwarsa ne wani Sanata ya nemi ayi masa jana’izar karramawa a jihar wanda har yanzu, bayan shekara guda kenan, babu wani abu da ya gudana abin da ya saka danginsa yanke shawarar binne sa da tallafin da gwamnatin jihar Oyo ta samar.