fidelitybank

Gwamnati ta yi mana alƙawarin ƙarya na binne Mahaifin mu – Iyalan Mutumin da ya zana tutar Najeriya

Date:

Iyalan Taiwo Michael Akinkunmi, mutumin da ya zana tutar Najeriya, sun ce sun gaji da jiran jana’izar karramawar da aka yi musu alƙawari, shekara guda bayan rasuwarsa yana da shekaru 87.

A maimokon jiran jana’izar da aka yi musu alƙwari, iyalan sun ce za su binne Akinkunmi, wanda aka fi sani da “Mr. Flag” a wannan makon a jihar Oyo, inda ya ke zauna.

Duk da fatan jana’izar da jihar ta yi, ɗan Akinkunmi, Akinwumi Akinkunmi, ya bayyana cewa iyalan sun zaɓi su binne shi, tare da tallafin da gwamnatin jihar Oyo ta bayar.

“Dole ne mu yi masa jana’izar da ya dace,” Akinwumi ya shaida wa BBC Focus on Africa podcast.

Taiwo Akinkunmi, wanda ya zana tutar Najeriya kafin ƙasar ta samu ‘yancin kai a 1960, mutum ne mai tawali’u.

An haife shi ne a Jihar Ibadan kuma ya yi aiki a matsayin ma’aikacin gwamnati a ma’aikatar noma har zuwa lokacin da ya yi ritaya a shekarar 1994.

Duk da irin gudunmawar da Akinkunmi ya bayar, har zuwa lokacin da Nijeriya ta cika shekaru 50 da samun ‘yancin kai, ba a san shi ba a matsayin ɗaya daga cikin fitattun ‘yan Nijeriya 50.

Bayan rasuwarsa ne wani Sanata ya nemi ayi masa jana’izar karramawa a jihar wanda har yanzu, bayan shekara guda kenan, babu wani abu da ya gudana abin da ya saka danginsa yanke shawarar binne sa da tallafin da gwamnatin jihar Oyo ta samar.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp