fidelitybank

Gwamnati ta yi gargaɗin sake samun mummunar ambaliya a jihohi biyu

Date:

Ministan Albarkatun ruwa da tsaftar muhalli, Joseph Utsev ya yi gargaɗin sake samun mummunar ambaliya a kogunan Neja da Benue.

Yayin da yake jawabi ga taron menama labarai a Abuja, babban birnin ƙasar, Ministan ya ce an samu ƙaruwar ruwan da ke ƙwarara a kogunan biyu zuwa yankin Naija Delta da ke kudancin ƙasar.

‘A yayin da muke jajanta wa al’ummomin jihohin Borno da Yobe da Jigawa da Bauchi da sauran jihohin da suka fuskanci ambaliya, muna ƙara jan hankalin ‘yan ƙasar game da yiwuwar sake fuskantar wata ambaliyar daga kogunan Benue da Neja da wasu yankunan yankin”, in ji ministan.

Kan haka ne mista Utsev ya yi kira ga mazauna yankin su ɗauki matakai domin kauce wa bala’in ambaliya a wasu sassan kudancin ƙasar.

Gargaɗin na zuwa ne a daidai lokacin da al’ummar birnin Maiduguri ke fuskantar mummunar ambaliya da ta auka wa birnin sakamakon fashewar madatsar ruwa ta Alau da ke wajen birnin.

Gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya ce lamarin ya shafi kusan mutum miliyan biyu.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp