fidelitybank

Gwamnati ta yi amfani da fasahar zamani wajen kawar da ‘yan ta’adda – Majalisa

Date:

Majalisar Dattijawa ta nemi gwamnati ta koma amfani da fasahar zamani a yanƙin da take yi da mayakan Boko Haram da ‘yan bindiga da sauran masu ɗauke da bindiga.

Hakan na ƙunshe cikin ƙudurin da Sanata Ali Ndume ya gabatar don ɗaukar matakin gaggawa kan harin da aka kai a yankin Gwoza da yake wakilta.

Bayan doguwar muhawara da aka kwashe sa’o’i ana yi tare da jajantawa kan harin, majalisar ta yarda cewa amfani da fasahar zamani a yaƙin zai kawo ƙarshen masu kai hare-haren ƙunar baƙin wake.

Haka kuma Majalisar ta amince a ƙara bayar da muhimmanci a yankin tafkin Chadi da dajin Sambisa da Kuma hayin dutsen Mandara.

Da yake bayar da tasa gudunmuwar, Sanata Adam Oshimole ya ce bai kamata a ƙara wa sojoji kuɗi ba da zimmar samar da makaman zamani da kuma fasaha, yana cewa an ba su kuɗaɗen da suke isassu a wannan lokaci.

Sai dai majalisar ta ƙi amincewa da bukatar tasa, inda mafi yawan mambobinta suka yi watsi da buƙatar.

Kazalika wasu daga cikin sanatocin sun nemi gwamnatin Najeriya ta haɗa hannu da kamfanonin tsaro masu zaman kansu domin ci gaba da yaƙi a yankunan Tafkin Chadi da dajin Sambisa da sauran wasu yankuna da ke fama da matsalar tsaro a Najeriya.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp