fidelitybank

Gwamnati ta sake tuhumar Kanu a kan ta’addanci

Date:

Gwamnatin Tarayya, ta sake gabatar da tuhumar ta’addanaci mai laifuka bakwai kan jagoran ‘yan awaren Biafra, Nnamdi Kanu, a gaban Babbar Kotun Tarayya.

A ranar 13 ga watan Oktoba ne Kotun Ɗaukaka Ƙara ta umarci a saki Kanu shugaban ƙungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB) daga gidan yari sakamakon abin da ta ce an gurfanar da shi ba bisa ƙa’ida ba.

Amma gwamnati ta ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙoli kan hukuncin na Kotun Ɗaukaka Ƙara.

Tun a watan Afrilun 2022 ne kotun ta yi watsi da tuhuma takwas cikin 15 da gwamnatin ke yi wa Kanu da suka haɗa da tayar da hankali da tsokanar Shugaba Muhammadu Buhari da cin amanar ƙasa.

Sai dai har yanzu ba a saki jagoran ba, inda yake ci gaba da zama a gidan yari a Abuja, babban birnin ƙasar.

Gwamnatin ta shigar da sabbin tuhumar ne yayin da ake jiran Kotun Ƙoli ta fara sauraron ƙarar da ta ɗaukaka kan hukuncin da ya ce a saki Kanu.

A watan Yunin 2021 ne gwamnati ta kama tare da sake gurfanar da Nnamdi Kanu a gaban kotu bayan ya gudu daga ƙasar ta hanyar karya dokokin belin da kotu ta bashi a gurfanarwar farko da aka yi masa.

Jami’an tsaro a Najeriya sun sha zargin ƙungiyar IPOB da kashe jami’ansu da kuma kai hare-hare kan mazauna yankin kudu maso gabashin ƙasar, inda ƙabilar Igbo suka fi rinjaye, yankin da take so ta kafa ƙasar Biafra idan ta ɓalle daga Najeriya.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp