Gwamnatin Tarayya, ta sake gabatar da tuhumar ta’addanaci mai laifuka bakwai kan jagoran ‘yan awaren Biafra, Nnamdi Kanu, a gaban Babbar Kotun Tarayya.
A ranar 13 ga watan Oktoba ne Kotun Ɗaukaka Ƙara ta umarci a saki Kanu shugaban ƙungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB) daga gidan yari sakamakon abin da ta ce an gurfanar da shi ba bisa ƙa’ida ba.
Amma gwamnati ta ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙoli kan hukuncin na Kotun Ɗaukaka Ƙara.
Tun a watan Afrilun 2022 ne kotun ta yi watsi da tuhuma takwas cikin 15 da gwamnatin ke yi wa Kanu da suka haɗa da tayar da hankali da tsokanar Shugaba Muhammadu Buhari da cin amanar ƙasa.
Sai dai har yanzu ba a saki jagoran ba, inda yake ci gaba da zama a gidan yari a Abuja, babban birnin ƙasar.
Gwamnatin ta shigar da sabbin tuhumar ne yayin da ake jiran Kotun Ƙoli ta fara sauraron ƙarar da ta ɗaukaka kan hukuncin da ya ce a saki Kanu.
A watan Yunin 2021 ne gwamnati ta kama tare da sake gurfanar da Nnamdi Kanu a gaban kotu bayan ya gudu daga ƙasar ta hanyar karya dokokin belin da kotu ta bashi a gurfanarwar farko da aka yi masa.
Jami’an tsaro a Najeriya sun sha zargin ƙungiyar IPOB da kashe jami’ansu da kuma kai hare-hare kan mazauna yankin kudu maso gabashin ƙasar, inda ƙabilar Igbo suka fi rinjaye, yankin da take so ta kafa ƙasar Biafra idan ta ɓalle daga Najeriya.