fidelitybank

Gwamnati ta sake tuhumar Kanu a kan ta’addanci

Date:

Gwamnatin Tarayya, ta sake gabatar da tuhumar ta’addanaci mai laifuka bakwai kan jagoran ‘yan awaren Biafra, Nnamdi Kanu, a gaban Babbar Kotun Tarayya.

A ranar 13 ga watan Oktoba ne Kotun Ɗaukaka Ƙara ta umarci a saki Kanu shugaban ƙungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB) daga gidan yari sakamakon abin da ta ce an gurfanar da shi ba bisa ƙa’ida ba.

Amma gwamnati ta ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙoli kan hukuncin na Kotun Ɗaukaka Ƙara.

Tun a watan Afrilun 2022 ne kotun ta yi watsi da tuhuma takwas cikin 15 da gwamnatin ke yi wa Kanu da suka haɗa da tayar da hankali da tsokanar Shugaba Muhammadu Buhari da cin amanar ƙasa.

Sai dai har yanzu ba a saki jagoran ba, inda yake ci gaba da zama a gidan yari a Abuja, babban birnin ƙasar.

Gwamnatin ta shigar da sabbin tuhumar ne yayin da ake jiran Kotun Ƙoli ta fara sauraron ƙarar da ta ɗaukaka kan hukuncin da ya ce a saki Kanu.

A watan Yunin 2021 ne gwamnati ta kama tare da sake gurfanar da Nnamdi Kanu a gaban kotu bayan ya gudu daga ƙasar ta hanyar karya dokokin belin da kotu ta bashi a gurfanarwar farko da aka yi masa.

Jami’an tsaro a Najeriya sun sha zargin ƙungiyar IPOB da kashe jami’ansu da kuma kai hare-hare kan mazauna yankin kudu maso gabashin ƙasar, inda ƙabilar Igbo suka fi rinjaye, yankin da take so ta kafa ƙasar Biafra idan ta ɓalle daga Najeriya.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp